• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Daga Mali Sun Kashe Mutane 17 A Sakkwato

by Sadiq
1 year ago
Sakkwato

Jami’an tsaro a Jihar Sakkwato, sun bayyana cewar wasu ‘yan bindiga daga kasar Mali da suka tsallako iyaka daga Nijar sun kashe mutane 17 ciki har da jami’an sabuwar rundunar tsaro da gwamnatin jihar ta Kafa guda biyar.

Hare-haren dai sun faru a karamar hukumar Gudu mai iyaka da Jamhuriyar Nijar.

  • Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Kashi 81.69 Cikin Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyinsu Sun Nuna Damuwa Matuka Game Da Karfafa Alakar Soji Tsakanin Japan Da Amurka
  • DA DUMI-DUMI: ‘Yansanda Sun Daƙile Harin Bom a Legas

Kantoman karamar hukumar, Umar Maikano Ballee ya shaida wa manema labarai cewa hare-haren na ‘yan bindigar da ake kira lakurawa sun fara ne daga ranar Asabar.

A cewarsa sun kai hari biyu – garin karfen China, inda suka harbi manoma shida har guda hudu suka mutu nan take sai biyu da ke jinya a asibiti, guda a cikinsu rai ya yi halinsa a ranar Talata.

“Bayan kwana daya suka sake zuwa karfen sarki suka kashe mutum takwas, cikinsu akwai jami’an tsaron al’umma, da sauran mutanen gari hudu.” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

Kantoman ya kara da cewa suna zargin lakurawa masu shigowa daga Mali da kai hare-haren biyu.

“Sun shigo yankin ranar Alhamis da karfe shida na yamma, sun shigo ta gefen jimajimi, daga nan suka zo suka tsallaka wannan titin na kurdula suka tsallaka nan garin Jeji suka tsallaka kokotau suka tsallaka wannan dajin na karfen sarki.” kamar yadda ya bayyana.

Ya ce ba shi da masaniya kan abin da ya hada lakurawan da mutanen garuruwan sai dai ya ce “abin da muka sani sun zo wadannan kauyuka suna kora shanun mutane, a kwana na biyu sai suka shiga suna harbin manoma.”

Balle, ya ce akwai jami’an tsaro da ke kare jama’a sai dai a ranar da lamarin ya faru, an yi ruwan sama, abin da ya kawo cikas ga jami’an tsaron su kai ga kauyuka a motocinsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gaza
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Next Post
Ba Mu Da Hannu A Kisan Isma’il Haniyeh – Amurka

Ba Mu Da Hannu A Kisan Isma'il Haniyeh – Amurka

LABARAI MASU NASABA

gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Sakkwato

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.