• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Na Sake Hada Gungu Duk Da Farmakin Sojoji

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Sojoji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da hare-hare gami da fatattakar da sojoji ke yi wa ‘yan bindiga, ga dukkan alamu ‘yan bindigar dake yankin Arewa maso yammacin Nijeriya na ci gaba da hadewa suna kai hare-hare a Maradun da Zuru, a Zamfara da kuma Karamar Hukumar Kankara a Katsina cikin kwanaki 3 da suka gabata.

LEADERSHIP Weekend ta ruwaito daga majiya mai tushe ta rundunar ‘yansandan Jihar Zamfara cewa kwanaki ukun da suka gabata an fuskanci matsi sakamakon hare-haren da ‘yan bindiga ke kaiwa.

  • Matsalar Ruwan Sha: Yara 9 Sun Mutu A Kwale-Kwale, 12 Sun Bace A Zamfara
  • Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Sake Kutsawa Garin Abuja, Sun Sace Mutane 4

‘Yan bindiga sun kuma kai hari tare da kashe sojoji 6, biyu daga cikinsu jami’ai ne a karamar hukumar Shiroror ta jihar Neja, jihar ta Arewa ta tsakiya wacce ke kan iyaka da Kaduna da Kebbi, dukkansu jihohin Arewa maso Yamma.

Sojojin Nijeriya tare da hadin gwiwar jami’an tsaron farin kaya (DSS) sun dakile harin ‘yan ta’adda a Jihar Sokoto, inda suka kashe bakwai daga cikin ‘yan ta’addan.

A wata sanarwa da rundunar sojin Nijeriya ta fitar akan shafinta na D ta ce dakarun da ke jiran ko-ta-kwana sun kama wasu ‘yan ta’adda dauke da makamai a wani farmaki da suka kai a yankin Modachi na Karamar Hukumar Isa ta Jihar Sakkwato.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

Sanarwar ta ce dakarun da ke aikin hadin gwiwa sun kashe 7 daga cikin ‘yan ta’adda tare da kwato manyan tarin makamai.

‘Yan ta’adda da ke wucewa da babura da dama, jami’an tsaro sun yi artabu da su, lamarin da ya kai ga halaka ‘yan ta’adda bakwai.

Sannan Sojojin sun kwato bindigogi kirar AK-47 bakwai, babura hudu, wayoyin hannu biyu, da adduna hudu.

Sojojin Nijeriya a cikin makonni uku da suka gabata sun kashe ‘yan ta’adda 31 a yankin Arewa maso Yamma, gami da kwato wasu makamai tare da rasa sojoji 7 a wani harin kwantan bauna.

A harin na baya-bayan nan, an bayyana cewa wasu ‘yan bindiga a Katsina sun kashe wani jami’in runduna ta 17 na sojojin Nijeriya, Manjo A.G Mohammed.

Marigayi Mohammed mamba ne na Operation Hadarin Daji kuma kwamandan da ke kula da ayyukan soji a Bantumaki, Dan Ali da Kankara a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaRashin TsaroTa'addancin 'yan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Cutar Kyanda Ta Yi Ajalin Mutum 42 A Adamawa

Next Post

Kyawawan ‘Yan Mata Da Suke Shiga Harkar Fim Suna Bata Rayuwarsu -Kyauta Dillaliya

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

1 month ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

2 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

2 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

2 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

2 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
Next Post
Kyawawan ‘Yan Mata Da Suke Shiga Harkar Fim Suna Bata Rayuwarsu -Kyauta Dillaliya

Kyawawan 'Yan Mata Da Suke Shiga Harkar Fim Suna Bata Rayuwarsu -Kyauta Dillaliya

LABARAI MASU NASABA

gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.