ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Na Sake Hada Gungu Duk Da Farmakin Sojoji

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Sojoji

Duk da hare-hare gami da fatattakar da sojoji ke yi wa ‘yan bindiga, ga dukkan alamu ‘yan bindigar dake yankin Arewa maso yammacin Nijeriya na ci gaba da hadewa suna kai hare-hare a Maradun da Zuru, a Zamfara da kuma Karamar Hukumar Kankara a Katsina cikin kwanaki 3 da suka gabata.

LEADERSHIP Weekend ta ruwaito daga majiya mai tushe ta rundunar ‘yansandan Jihar Zamfara cewa kwanaki ukun da suka gabata an fuskanci matsi sakamakon hare-haren da ‘yan bindiga ke kaiwa.

  • Matsalar Ruwan Sha: Yara 9 Sun Mutu A Kwale-Kwale, 12 Sun Bace A Zamfara
  • Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Sake Kutsawa Garin Abuja, Sun Sace Mutane 4

‘Yan bindiga sun kuma kai hari tare da kashe sojoji 6, biyu daga cikinsu jami’ai ne a karamar hukumar Shiroror ta jihar Neja, jihar ta Arewa ta tsakiya wacce ke kan iyaka da Kaduna da Kebbi, dukkansu jihohin Arewa maso Yamma.

ADVERTISEMENT

Sojojin Nijeriya tare da hadin gwiwar jami’an tsaron farin kaya (DSS) sun dakile harin ‘yan ta’adda a Jihar Sokoto, inda suka kashe bakwai daga cikin ‘yan ta’addan.

A wata sanarwa da rundunar sojin Nijeriya ta fitar akan shafinta na D ta ce dakarun da ke jiran ko-ta-kwana sun kama wasu ‘yan ta’adda dauke da makamai a wani farmaki da suka kai a yankin Modachi na Karamar Hukumar Isa ta Jihar Sakkwato.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Sanarwar ta ce dakarun da ke aikin hadin gwiwa sun kashe 7 daga cikin ‘yan ta’adda tare da kwato manyan tarin makamai.

‘Yan ta’adda da ke wucewa da babura da dama, jami’an tsaro sun yi artabu da su, lamarin da ya kai ga halaka ‘yan ta’adda bakwai.

Sannan Sojojin sun kwato bindigogi kirar AK-47 bakwai, babura hudu, wayoyin hannu biyu, da adduna hudu.

Sojojin Nijeriya a cikin makonni uku da suka gabata sun kashe ‘yan ta’adda 31 a yankin Arewa maso Yamma, gami da kwato wasu makamai tare da rasa sojoji 7 a wani harin kwantan bauna.

A harin na baya-bayan nan, an bayyana cewa wasu ‘yan bindiga a Katsina sun kashe wani jami’in runduna ta 17 na sojojin Nijeriya, Manjo A.G Mohammed.

Marigayi Mohammed mamba ne na Operation Hadarin Daji kuma kwamandan da ke kula da ayyukan soji a Bantumaki, Dan Ali da Kankara a jihar.

Bindiga
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Kyawawan ‘Yan Mata Da Suke Shiga Harkar Fim Suna Bata Rayuwarsu -Kyauta Dillaliya

Kyawawan 'Yan Mata Da Suke Shiga Harkar Fim Suna Bata Rayuwarsu -Kyauta Dillaliya

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.