• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Abuja, Sun Yi Garkuwa Da Mutane 9

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Abuja, Sun Yi Garkuwa Da Mutane 9
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan bindiga da suka kai kimanin 20 a daren Juma’a da misalin karfe 11:30 na dare sun kai farmaki rukunin gidaje na Grow Homes da ke Kuchibiyi a yankin Kubwa a babban birnin tarayya Abuja, inda suka yi garkuwa da wasu mazauna unguwar kimanin tara da suka hada da mata da kananan yara.

Wani mazaunin unguwar da ya bayyana sunansa da Hassan, ya bayyana cewa an yi garkuwa da mutanen ne daga wasu gidaje guda biyu kuma lamarin ya haifar da firgici a yankin.

  • Zulum Ya Ziyarci Iyalan Masuntan Da Boko Haram Ta Hallaka A Borno
  • Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Yi Wa Mace Kurma Fyade A Jihar Nasarawa 

“A jiya da misalin karfe 11:30 na dare wasu ‘yan bindiga da yawa sun zo domin kai farmaki a rukunin gidaje na Grow Homes da ke Kuchibiyi. Mun ji karar harbe-harbe, an shiga firgici a daukacin yankin.

“Da safiyar yau, mun je gidan, muka samu labarin cewa ‘yan bindigar sun kai kimanin 20. Sun tashi daga wani gida zuwa wancan suna korar mazauna yankin. Sun kuma yi garkuwa da akalla mutane tara da suka hada da yara da mata daga wasu gidaje biyu.

“Sun tsere ne cikin daji wanda ya danganta al’ummar kauyen Paze. Tun da safe ‘yansanda da jami’an tsaro sun fara bincike a daji don ganin ko za su iya kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kakakin rundunar ‘yansandan babban birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, yayin da ta ke tabbatar da afkuwar lamarin, ta ce ‘yansanda da jami’an tsaro na kokarin ceto mutane.

“Bayan samun kiran gaggawa nan take muka tura mutanenmu wurin. Sai dai wadanda ake zargin sun tsere zuwa daji.

“Rundunar ‘yansanda da jami’an tsaro na ci gaba da bincike a yankin domin ganin an ceto su ba tare da wani rauni ba,” in ji ta.

Ta kuma bukaci mazauna yankin da kada su firgita, inda ta yi kira gare su da su taimaka wa ‘yansanda da sahihan bayanan da za su kai ga cafke maharan.

“Muna kira ga mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu tare da bayar da bayanai masu amfani da za su iya kai ga cafke wadannan masu laifin cikin gaggawa,” in ji SP Adeh.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaGarkuwa Da MutaneKubwaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zulum Ya Ziyarci Iyalan Masuntan Da Boko Haram Ta Hallaka A Borno

Next Post

Dan Shekara 13 Ya Harbe Karamar Yarinya Da Bindiga A Ogun

Related

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2

7 days ago
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

3 weeks ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

3 weeks ago
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

4 weeks ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

4 weeks ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

4 weeks ago
Next Post
Dan Shekara 13 Ya Harbe Karamar Yarinya Da Bindiga A Ogun

Dan Shekara 13 Ya Harbe Karamar Yarinya Da Bindiga A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.