• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Abuja, Sun Yi Garkuwa Da Mutane 9

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Abuja, Sun Yi Garkuwa Da Mutane 9
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan bindiga da suka kai kimanin 20 a daren Juma’a da misalin karfe 11:30 na dare sun kai farmaki rukunin gidaje na Grow Homes da ke Kuchibiyi a yankin Kubwa a babban birnin tarayya Abuja, inda suka yi garkuwa da wasu mazauna unguwar kimanin tara da suka hada da mata da kananan yara.

Wani mazaunin unguwar da ya bayyana sunansa da Hassan, ya bayyana cewa an yi garkuwa da mutanen ne daga wasu gidaje guda biyu kuma lamarin ya haifar da firgici a yankin.

  • Zulum Ya Ziyarci Iyalan Masuntan Da Boko Haram Ta Hallaka A Borno
  • Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Yi Wa Mace Kurma Fyade A Jihar Nasarawa 

“A jiya da misalin karfe 11:30 na dare wasu ‘yan bindiga da yawa sun zo domin kai farmaki a rukunin gidaje na Grow Homes da ke Kuchibiyi. Mun ji karar harbe-harbe, an shiga firgici a daukacin yankin.

“Da safiyar yau, mun je gidan, muka samu labarin cewa ‘yan bindigar sun kai kimanin 20. Sun tashi daga wani gida zuwa wancan suna korar mazauna yankin. Sun kuma yi garkuwa da akalla mutane tara da suka hada da yara da mata daga wasu gidaje biyu.

“Sun tsere ne cikin daji wanda ya danganta al’ummar kauyen Paze. Tun da safe ‘yansanda da jami’an tsaro sun fara bincike a daji don ganin ko za su iya kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

Kakakin rundunar ‘yansandan babban birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, yayin da ta ke tabbatar da afkuwar lamarin, ta ce ‘yansanda da jami’an tsaro na kokarin ceto mutane.

“Bayan samun kiran gaggawa nan take muka tura mutanenmu wurin. Sai dai wadanda ake zargin sun tsere zuwa daji.

“Rundunar ‘yansanda da jami’an tsaro na ci gaba da bincike a yankin domin ganin an ceto su ba tare da wani rauni ba,” in ji ta.

Ta kuma bukaci mazauna yankin da kada su firgita, inda ta yi kira gare su da su taimaka wa ‘yansanda da sahihan bayanan da za su kai ga cafke maharan.

“Muna kira ga mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu tare da bayar da bayanai masu amfani da za su iya kai ga cafke wadannan masu laifin cikin gaggawa,” in ji SP Adeh.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaGarkuwa Da MutaneKubwaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zulum Ya Ziyarci Iyalan Masuntan Da Boko Haram Ta Hallaka A Borno

Next Post

Dan Shekara 13 Ya Harbe Karamar Yarinya Da Bindiga A Ogun

Related

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

2 days ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi
Da ɗumi-ɗuminsa

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

3 days ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

3 days ago
Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

3 days ago
Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba

6 days ago
Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

6 days ago
Next Post
Dan Shekara 13 Ya Harbe Karamar Yarinya Da Bindiga A Ogun

Dan Shekara 13 Ya Harbe Karamar Yarinya Da Bindiga A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.