ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Abuja, Sun Yi Garkuwa Da Mutane 9

by Sadiq
3 years ago
Abuja

Wasu ‘yan bindiga da suka kai kimanin 20 a daren Juma’a da misalin karfe 11:30 na dare sun kai farmaki rukunin gidaje na Grow Homes da ke Kuchibiyi a yankin Kubwa a babban birnin tarayya Abuja, inda suka yi garkuwa da wasu mazauna unguwar kimanin tara da suka hada da mata da kananan yara.

Wani mazaunin unguwar da ya bayyana sunansa da Hassan, ya bayyana cewa an yi garkuwa da mutanen ne daga wasu gidaje guda biyu kuma lamarin ya haifar da firgici a yankin.

  • Zulum Ya Ziyarci Iyalan Masuntan Da Boko Haram Ta Hallaka A Borno
  • Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Yi Wa Mace Kurma Fyade A Jihar Nasarawa 

“A jiya da misalin karfe 11:30 na dare wasu ‘yan bindiga da yawa sun zo domin kai farmaki a rukunin gidaje na Grow Homes da ke Kuchibiyi. Mun ji karar harbe-harbe, an shiga firgici a daukacin yankin.

ADVERTISEMENT

“Da safiyar yau, mun je gidan, muka samu labarin cewa ‘yan bindigar sun kai kimanin 20. Sun tashi daga wani gida zuwa wancan suna korar mazauna yankin. Sun kuma yi garkuwa da akalla mutane tara da suka hada da yara da mata daga wasu gidaje biyu.

“Sun tsere ne cikin daji wanda ya danganta al’ummar kauyen Paze. Tun da safe ‘yansanda da jami’an tsaro sun fara bincike a daji don ganin ko za su iya kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

Kakakin rundunar ‘yansandan babban birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, yayin da ta ke tabbatar da afkuwar lamarin, ta ce ‘yansanda da jami’an tsaro na kokarin ceto mutane.

“Bayan samun kiran gaggawa nan take muka tura mutanenmu wurin. Sai dai wadanda ake zargin sun tsere zuwa daji.

“Rundunar ‘yansanda da jami’an tsaro na ci gaba da bincike a yankin domin ganin an ceto su ba tare da wani rauni ba,” in ji ta.

Ta kuma bukaci mazauna yankin da kada su firgita, inda ta yi kira gare su da su taimaka wa ‘yansanda da sahihan bayanan da za su kai ga cafke maharan.

“Muna kira ga mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu tare da bayar da bayanai masu amfani da za su iya kai ga cafke wadannan masu laifin cikin gaggawa,” in ji SP Adeh.

MASU ALAKA

Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

May 5, 2026
Next Post
Dan Shekara 13 Ya Harbe Karamar Yarinya Da Bindiga A Ogun

Dan Shekara 13 Ya Harbe Karamar Yarinya Da Bindiga A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.