ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Abuja, Sun Yi Garkuwa Da Mutane 9

by Sadiq
3 years ago
Abuja

Wasu ‘yan bindiga da suka kai kimanin 20 a daren Juma’a da misalin karfe 11:30 na dare sun kai farmaki rukunin gidaje na Grow Homes da ke Kuchibiyi a yankin Kubwa a babban birnin tarayya Abuja, inda suka yi garkuwa da wasu mazauna unguwar kimanin tara da suka hada da mata da kananan yara.

Wani mazaunin unguwar da ya bayyana sunansa da Hassan, ya bayyana cewa an yi garkuwa da mutanen ne daga wasu gidaje guda biyu kuma lamarin ya haifar da firgici a yankin.

  • Zulum Ya Ziyarci Iyalan Masuntan Da Boko Haram Ta Hallaka A Borno
  • Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Yi Wa Mace Kurma Fyade A Jihar Nasarawa 

“A jiya da misalin karfe 11:30 na dare wasu ‘yan bindiga da yawa sun zo domin kai farmaki a rukunin gidaje na Grow Homes da ke Kuchibiyi. Mun ji karar harbe-harbe, an shiga firgici a daukacin yankin.

ADVERTISEMENT

“Da safiyar yau, mun je gidan, muka samu labarin cewa ‘yan bindigar sun kai kimanin 20. Sun tashi daga wani gida zuwa wancan suna korar mazauna yankin. Sun kuma yi garkuwa da akalla mutane tara da suka hada da yara da mata daga wasu gidaje biyu.

“Sun tsere ne cikin daji wanda ya danganta al’ummar kauyen Paze. Tun da safe ‘yansanda da jami’an tsaro sun fara bincike a daji don ganin ko za su iya kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

Kakakin rundunar ‘yansandan babban birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, yayin da ta ke tabbatar da afkuwar lamarin, ta ce ‘yansanda da jami’an tsaro na kokarin ceto mutane.

“Bayan samun kiran gaggawa nan take muka tura mutanenmu wurin. Sai dai wadanda ake zargin sun tsere zuwa daji.

“Rundunar ‘yansanda da jami’an tsaro na ci gaba da bincike a yankin domin ganin an ceto su ba tare da wani rauni ba,” in ji ta.

Ta kuma bukaci mazauna yankin da kada su firgita, inda ta yi kira gare su da su taimaka wa ‘yansanda da sahihan bayanan da za su kai ga cafke maharan.

“Muna kira ga mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu tare da bayar da bayanai masu amfani da za su iya kai ga cafke wadannan masu laifin cikin gaggawa,” in ji SP Adeh.

MASU ALAKA

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

May 5, 2026
Gwamnatin Jigawa Ta Bayar Da Umarnin Bincikar Tsohon Gwamnan Jihar Badaru
Siyasa

Gwamnatin Jigawa Ta Bayar Da Umarnin Bincikar Tsohon Gwamnan Jihar Badaru

April 25, 2026
Next Post
Dan Shekara 13 Ya Harbe Karamar Yarinya Da Bindiga A Ogun

Dan Shekara 13 Ya Harbe Karamar Yarinya Da Bindiga A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.