Wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kashe wani ɗan kasuwa mai shekaru 45, Alhaji Dauda Ismail, a garin Okuta da ke ƙaramar hukumar Baruten, a Jihar Kwara.
Rahotanni sun nuna cewa maharan sun sace Alhaji Dauda wanda ke kasuwancin kayan gona, kuma suka kashe shi a ranar Litinin a unguwar Takare da ke Okuta.
- Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
- Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta
Kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Kwara, Toun Ejire-Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ta fitar da yammacin ranar Talata.
Ta ce ‘yansanda sun kashe ɗaya daga cikin masu garkuwar a musayar wuta.
Ta ƙara da cewa wani ɗan banga mai suna Haruna Tasusuno shi ma an harbe shi a yayin fafatawar, kuma an garzaya da shi asibitin garin Okuta, inda aka tabbatar da mutuwarsa.
A cewar sanarwar, a ranar 22 ga watan Yuni, 2025, da misalin ƙarfe 10:40 na dare, wasu mutane huɗu ɗauke da bindigu sun kai farmaki gidan Alhaji Dauda, inda suka yi harbe-harbe sannan suka sace shi suka tafi da shi zuwa wani waje da ba a sani ba.
Nan da nan jami’an ‘yansanda, sojoji, ‘yan banga da masu farauta suka haɗa tawaga domin shiga daji don ceto mutumin.
Washegari da safe, ranar 23 ga watan Yuni, da misalin ƙarfe 7 na safe, tawagar ta haɗu da masu garkuwar a ƙauyen Korori.
Sai da aka yi musayar wuta, inda aka kashe ɗaya daga cikinsu, aka ƙwato bindiga ƙirar AK-47 mai harsashi 13.
Sauran kuwa suka tsere cikin daji, kuma ana ci gaba da nemansu.
Abin takaici, ɗan banga Haruna Tasusuno ya samu rauni sakamakon harbi, inda aka garzaya da shi asibiti kuma aka tabbatar da rasuwarsa daga baya.
An samu Alhaji Dauda kwance a daji cikin jini da raunukan sara da adda a jikinsa, kuma likita ya tabbatar da cewa ya rasu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp