• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 29, Sun Sace Babura Sama Da 152 A Yankin Da Ake Hako Ma’adanai A Zamfara

by Sulaiman and Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 29, Sun Sace Babura Sama Da 152 A Yankin Da Ake Hako Ma’adanai A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne, sun kai hari a inda ake hakar ma’adanai a yankin ‘Yar-Nasarawa a cikin karamar hukumar Maru da ke jihar Zamfara.

A lokacin harin, ‘yan bindigar sun kuma hallaka mutane 29 da sace Babura 152.

  • Mun Yi Iya Kokarinmu Wajen Shugabancin Nijeriya —Buhari

Wajen hakar ma’adanan, tana daura da yankunan Malele, Ruwan Tofa da kuma ‘Yansawayu da ke kan hanyar masarautar Dansadau.

An ruwaito cewa, ‘yan bindigar sun kai a harin ne akan baburansu da adadi masu yawa a yayin da ma’aikata sama da 300 ke kan hakar ma’adanai a lokacin.

Rahotanni sun ce, duk da haramta hakar ma’adanai a jihar, wasu mutane sun cigaba da hakar ta haramtacciyar hanya a wasu sassan jihar.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

A cewar majiyoyin, tawagar ‘yan ta’adda biyu ne suka kai harin na hadin guiwa da Lawali Damina da Ali Kachalla ke jagoranta.

Wani mazaunin a yankin Ruwan Tofa wanda ya tsallake Rijiya da baya, ya bayyana cewa, wadanda suka rasa rayukansu a lokacin harin, an yi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanadar.

A cewarsa, gungun ‘yan bindigar sun kai hari ne da kimanin karfe 4 na yamma, a yayin da masu hakar ma’adanai sama da 300 ke wurin a lokacin.

Ya ce, ‘yan bindigar sun kuma yi awon gaba da babura 152.

A cewarsa, amma a yanzu al’amura sun daiddai duk da cewa, babu jami’in tsaro ko daya da yazo yankunan.

Amma da aka tuntubi gwamnati da kuma rundunar ‘yansandan jihar kan harin, rundunar ta ce, ba a kawo mata wani rahoto kan wannan harin ba.

Sai dai, an ruwaito kwamishinan kula da harkokin tsaro da kula da harkokin cikin gida na jihar, MamanTsafe ya ce, yana sane da wajen hakar ma’adanan da ake magana akai, amma bai da wata masaniya kan harin, amma zai bincika.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gidan Da Ganduje Zai Tare Na Miliyoyin Naira Ya Yi Gobara A Kano

Next Post

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Habasha

Related

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

19 minutes ago
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet
Labarai

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

8 hours ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

13 hours ago
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

14 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

14 hours ago
Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
Labarai

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

14 hours ago
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Habasha

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Habasha

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

July 5, 2025
In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

July 4, 2025
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

July 4, 2025
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

July 4, 2025
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

July 4, 2025
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

July 4, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

July 4, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

July 4, 2025
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

July 4, 2025
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.