ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Yi Iya Kokarinmu Wajen Shugabancin Nijeriya —Buhari

by Sadiq
3 years ago
Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya gode wa ministocinsa da ma’aikatan fadar shugaban kasa da suka yi aiki tare da shi cikin shekaru takwas da suka gabata.

Shugaban kasar wanda zai mika wa zababben shugaban kasa, Bola Tinubu mulki a ranar 29 ga watan Mayu, ya ce yana alfahari da cewa shi da mukarrabansa sun bai ‘yan Nijeriya iya gudunmawarsu.

  • Tabbas Za’a Karyata Jita-Jitar Dake Shafawa Jihar Tibet Bakin Fenti
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 96 Da Ake Zargi Da Aikata Laifuka A Kano

A taron majalisar zartaswa ta tarayya (FEC) da aka gudanar a zauren majalisar dokoki, shugaban ya mika godiyarsa ga dukkanin ministocin bisa jajircewar da suka yi wajen cimma manufofin gwamnatin, inda ya bukaci a marawa shugaban kasa mai jiran gado baya.

ADVERTISEMENT

“Ina alfahari da cewa mun yi iya Kokarinmu,” an ruwaito shugaban kasar yana fadar haka a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Femi Adesina ya fitar.

Shugaban ya umarci ministocin da su gyara ayyukansu tare da kaucewa gaggawar da ka iya kawo cikas ga ayyukan alheri da suka yi tsawon shekaru.

LABARAI MASU NASABA

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

“Sakamakon shekarun da muka yi tare, tsawon shekaru bakwai da rabi, mun bambanta kan batutuwa da yawa. Ina rokon mu fahimci cewa wadannan mukamai sun kasance na gama gari ne, kuma babu wanda ya isa ya ci gaba da koke-koke, ko ci gaba da wadannan bambance-bambance.

“Ga wadanda ba za su kasance cikin gwamnati kai tsaye ba, na san ina daya daga cikin irin wadannan, ina rokon mu ci gaba da bayar da goyon bayanmu, ta kowace hanya, idan babbar jam’iyyarmu ta kira mu, wacce ta ba mu damar tsayawa, kuma dole ne mu ci gaba da mara mata baya ta kowace hanya da za mu iya,” in ji shi.

Shugaban ya danganta duk wani kyakkyawan aiki da fatan alheri da gwamnatin ta samu da taimakon Allah, inda ya kara da cewa, “Ina kuma gode wa Allah da Ya ba mu karfin gwiwa da ya hada mu baki daya.

“Zan kuma yi farin cikin yin abubuwa da dama da ban samu ba tun ranar 29 ga watan Mayu, 2015, daya daga cikin irin wannan shi ne lokacin da na fi so na kula da shanuna.

“Ina yi mana fatan alheri kuma ina fatan mu ji labari mai dadi a duk lokacin da aka ambaci sunayenmu. Na gode kuma Allah ya albarkaci Tarayyar Nijeriya,” in ji shi.

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Next Post
Kwana 4 Ga Rantsuwa: Yadda Shugabannin Duniya Ke Tururuwar Rantsar Da Tinubu

Kwana 4 Ga Rantsuwa: Yadda Shugabannin Duniya Ke Tururuwar Rantsar Da Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.