• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji Da ‘Yansanda 154 A Shekara Guda

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohuwa Mai Shekara 120 A Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan bindiga dadi da ke cin karensu babu babbaka sun kashe a kalla jami’an sojoji da ‘yansanda 154 a cikin shekara daya.

Binciken LEADERSHIP ya gano cewa a tsakannin watan Maris na 2023 zuwa Maris din 2024, jami’an ‘yansanda 90 ne aka kashe, yayin da kuma jami’an sojoji su 64 suka rasa rayukansu sakamakon aikace-aikacen ‘yan bindiga dadi.

  • Sin Ta Bayyana Rashin Jin Dadi Kan Binciken Da Eu Ta Yiwa Wasu Kamfanonin Sin Masu Samar Da Wasu Hajoji
  • Samun Tunanin Kashin Kai Zai Tabbatar Da Damar Ci Gaba

Bugu da kari, barnar ‘yan bindigan ya kai ga shafan wasu ‘yan kungiyan Sa-kai a karamar hukumar Mariga ta Jihar Neja, inda ‘yan sa-kai mutum 30 suka rasa rayukansu.

LEADERSHIP ta iya fahimtar cewa an kafa ‘yan sa-kai ne da nufin su yaki ‘yan fash-in daji da ‘yan bindiga dadi ta hanyar yin hadin guiwa da jama’an tsaro wajen ya-kar ‘yan fashin daji a yankunansu.

Wata majiya ta ce ‘yan fashin dajin sun farmaki mambobin kungiyar ‘yan sa-kai ne wadanda suke kan aikin bin sawun ‘yan fashin daji biyo bayan da suka yi garkuwa da wasu manoma a Dogon Dawa.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Majiyar ta ce ‘yan sa-kai na kokarin bibiyar takun ‘yan bindigan ne zuwa ma-boyarsu, inda suka auka tare da da kashe 30 a cikin ‘yan sa-kan gami da jikkata wasu da dama.

Shugaban karamar hukumar Mariga, Abbas Kasuwar Garba, ya tabbatar da faruwar lamarin tare da nuna matukar damuwa dangane da cewa mazauna yankunan na kokarin tsunduma gudanar da harkokin noma sai kuma mummunar annobar kai hare-hare na neman kara jefa su cikin halin firgici.

Ya ce a baya yankin na morar zaman lafiya don haka ne ya yi kira ga gwamnati da ta yi duk mai yiyuwa wajen shawo kan matsalar tsaron da ke barazana ga yankin.

A bangaren sojoji kuwa, mummunar hare-haren sun wakana ne a watan Agustan 2023 da Maris 2024 a jihohin Neja da Delta.

Na ‘yansandan Nijeriya kuwa, babban harin da ya wakana shi ne, wanda lokacin da ‘yan bindiga dadi suka yi kwautan bauna tare da hallaka babban jami’in dan-sanda (DPO), Bako Angbanshin tare da yin gunduwa-gunduwa da gawarsa a yankin Odumude da ke karamar hukumar Ahoada ta gabas a Jihar Ribas. Sai bayan wata shida da faruwar lamarin ne aka iya gano gawarsa.

Jerin Kashe-kashen Da Aka Yi Wa ‘Yansanda a shekarar 2023

A ranar 5 ga watan Maris 2023, ‘yan bindiga dadi sun kashe dansanda da jikkata wasu biyu a Jihar Anambra.

Tsakanin ranakun 13 zuwa 18 na Maris, ‘yansanda I6 ne aka kashe a yankin Ngas-ki da Gafara a karamar hukumar Ngaski ta Jihar Kebbi, a Jihar Neja da a Jihar Imo.

A ranar 20 ga Maris, rundunar ‘yansanda ta tabbatar da cewa sojoji sun kashe mata jami’ai guda biyu a Jihar Taraba.

A ranar 26 ga Maris, ‘yan bindiga sun farmaki shingen bincike ‘yansanda, inda su-ka kashe ‘yansanda biyu a Jihar Inugu.

Ranar 6 ga Afrilu, ‘yansanda uku ne aka kashe a Edo da raunata wani guda.

Ranar 7 ga Afrilu, wasu ‘yan bindiga dadin da ba a gano su waye ba sun harbe dansanda har lahira a Marine Base Junction da ke Fatakwal.

A ranar 21 ga Afrilu, ‘yan bindiga dadi sun kashe jami’an ‘yansanda biyar a Jihar Imo.

A ranar 26 ga watan Afrilu, wasu da ake zargin ‘’yan Yahoo boy’ ne sun kashe dansanda a Ibadan.

A ranar 28 ga watan Afriku, dansanda, Sergeant Ifeanyi an kasheshi bayan da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da shi a Jihar Delta.

Ranar 3 ga Mayu, ‘yan bindigan sun fille kan wani mataimakin sufuretandan dan-sanda da aka bayyana sunansa da Linus a kan layin East da ke Ndiegoro a Aba ta Jihar Abiya.

A ranar 16 ga watan Mayu, ‘yansanda biyu ne aka kashe a lokacin da ‘yan bindiga suka kai hari ga tawagar jami’an Amurka a Anambra.

Ranar 20 ga Mayu, ‘yan bindiga sun harbe ‘yansanda biyu a Imo. A wannan rana, an rawaito cewa jami’an ‘yansanda biyu ne aka kashe a Ughelli a karamar huku-mar Ughelli ta arewa a Jihar Delta a wani barin wuta, yayin da wani ya jikkata.

A ranar 24 ga May, harbin ‘yan bindiga dadi ya kashe wani dansanda a Ebonyi.

A ranar 18 ga watan Yuni, dansanda daya ne ya rasa ransa a lokacin da ‘yan bin-diga suka farmaki tawagar tsohon gwamnan Jihar Imo, Rochas Okorocha a Jihar Imo.

Ranar 26 ga Yuli, rundunar ‘yansanda ta tabbatar da cewa an kai hari ga tawagar kwamishina har an kashe jami’an ‘yansanda biyu a Aba.

A ranar 23 ga Yuli, wasu da ake zargin ‘yan fashin daji ne sun kai hari ga jami’an ‘yansanda a lokacin da suke bakin aikin tsaida mutane domin bincike a shata-letalen Oleh da ke Jihar Delta, inda suka kashe ‘yansanda biyu tare da banka wa motarsu ta sintiri wuta.

A ranar 11 ga Agustan, ‘yan acaba sun dira kan wani dansanda, inda suka kasheshi a Legas.

A ranar 25 ga Agustan, ‘yan bindiga sun kashe jami’in dansanda mai mukamin sufeto tare da yin awun gaba da bindigarsa a Ribas.

A ranar 8 ga Sabumba ne ‘yan bindiga suka kai hari tare da kashe wani DPO, Bako Angbanshin a yankin Odumude da ke karamar hukumar Ahoada ta gabas a Jihar Ribas.

Ranar 19 ga Satumba, akalla ‘yansanda biyar ne aka kashe a wani harin da ‘yan bindiga suka kai musu a kudancin Jihar Imo.

Ranar 20 ga Satumba, wasu ‘yan bindiga sun hallaka jami’an ‘yansanda biyu a ji-har Inugu.

A ranar 14 ga Oktoba, ‘yan fashi da makami sun kashe jami’in dansandan Nijeriya mai suna Joseph Fidus a gidansa da ke Iyana Cele a yankin Sango ta Jihar Ogun.

A ranar 21 ga Oktoba, ‘yan fashin banki sun hallaka ‘yansanda hudu a Jihar Benu-wai.

Ranar 27 ga Oktoba, ‘yan bindiga dadi sun kashe ‘yansanda biyu a lokacin da suke kokarin yin wani kame a Aba.

Ranar 17 Nuwamba, ‘yan daba sun kashe ‘yansanda biyu da jikkata wani guda a Jihar Ebonyi.

A ranar 18 ga Nuwamba, ‘yansanda biyu ne suka bakwanci lahira a wani harin da ake zargin cewa mambobin IPOB ne suka aiwaar a shalkwatar ‘yansanda da ke Ebonyi.

Ranar 22 ga Nuwamba, an zargi wani jami’n soja da kashe wani jami’in dansanda a wani caji ofis din ‘yansanda da ke Jihar Adamawa.

A ranar 27 ga Nuwamba, wasu ‘yan bindiga dadi da ba a san ko su waye ba sun kashe ‘yansanda biyu a Ahaira Junction da ke karamar hukumar Ahaizu Mbaise a Jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jakadan Sin A Nijar Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar

Next Post

Kamfanin Sin Ya Sa Hannu Kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Habasha Don Samar Da Lantarki

Related

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

40 minutes ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

4 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

6 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

9 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

10 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

13 hours ago
Next Post
Kamfanin Sin Ya Sa Hannu Kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Habasha Don Samar Da Lantarki

Kamfanin Sin Ya Sa Hannu Kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Habasha Don Samar Da Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.