ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samun Tunanin Kashin Kai Zai Tabbatar Da Damar Ci Gaba

by CGTN Hausa
2 years ago
Tunani

A shekarun baya bayan nan, kasar Amurka tana ta neman yin karin tasiri a nahiyar Afirka. Bisa wannan yunkuri, ana ta samun dimbin rahotanni daga kafofin yada labarai na kasashen yamma dake nuna wai “Amurka da Sin na takara da juna a nahiyar Afirka”, da “ kasashen yamma na takara da kasashen Sin da Rasha, da wasu kasashen dake gabas ta tsakiya, don kwatar damar kulla huldar kawance tare da kasashen Afirka”, da dai sauransu daga kafofin yada labarai na kasashen yamma. Hakan na sa mutum tsammanin cewa, watakila kasashen Afirka ba za su iya kaucewa daukar wani bangare, a tsakanin karfin dake takara da juna a duniya ba. Sai dai abun tambaya a nan shi ne ko kasashen na Afirka suna son yin haka?

Wata kila a ki yin zabi, ko ma a magance yarda da ra’ayin maida kasashen yamma cibiyar duniya, da neman dakile saura, zai fi dacewa ga kasashen Afirka, don neman biyan bukatunsu na kare moriyar kai.

  • Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Shugaban Kasar Mozambique
  • Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Tare Da Takwaransa Na Indonesia

A wajen taron musayar ra’ayi tsakanin Sin da Afirka ta fannin wayewar kai karo na 3, da ya gudana a kwanan nan a birnin Beijing na Sin, masana da jami’ai na kasashen Afirka da na kasar Sin sun sake jaddada muhimmancin ra’ayin diplomasiyya na magance daukar wani bangare. Kana wannan ra’ayi ya zama daya da tunanin hadin gwiwar Sin da Afirka, wato maimakon nuna son kai da neman dakile saura, a bude kofa domin kowa ya iya halarta, da aiwatar da tunani na kasancewar dimbin bangarori masu fada a ji a duniya.

ADVERTISEMENT

Taron na wannan karo ya kunshi dandalin tattaunawa guda 2, daya ya shafi musayar ra’ayi cikin daidaito, kan al’adu da tunani na Sin da Afirka. Daya kuwa ya shafi musayar ra’ayin raya kasa, don aza harsashin hadin gwiwar nan gaba. Kana babbar ma’anar taron ita ce, kamar yadda Rahamtalla M. Osman, jakadan kungiyar tarayyar kasashen Afirka AU a kasar Sin ya fada, “Daidaita ra’ayi da magance bahaguwar fahimta, ta yadda za a karfafa fahimtar juna da girmama juna da hadin gwiwa, ta hanyar yin musayar ra’ayi”.

Nufinsa shi ne, ta hanyar tattaunawa, ake neman kawar da shingen tunani da ra’ayoyi marasa dacewa, da kasar Amurka da wasu kasashen dake yammacin duniya suka sanya wa kasashen Afirka da kasar Sin, da sauran kasashe masu tasowa. Ta yadda za a samu tunani na kai, da yiwuwar dogaro da kai, da samun ci gaban kasa mai dorewa.

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Irin wannan cudanyar ra’ayi mai daraja, ta sa ana ta samun tunani masu muhimmanci a tarukan musayar ra’ayi, tsakanin Sin da Afirka ta fannin wayewar kai, da aka taba gudanarwa a baya.

Misali, Rahamtalla M. Osman, jakadan kungiyar kasashen Afirka AU a kasar Sin, ya taba bayyanawa a madadin kungiyar AU cewa, ya kamata a daina ta da rikici tsakanin mabambantan wayewar kai, da neman tabbatar da kasancewarsu tare, da daina ganin al’adun wasu sun fi na wasu, tare da karfafa cudanya, da koyi da juna tsakanin wayin kai daban daban.

Sa’an nan a nasa bangare, shugaban cibiyar nazarin manufofin kasashen Afirka na kasar Kenya Peter Kagwanja, ya taba bayyana cewa, “Aikin zamanantar da kasar Sin, da yadda ake neman zamanantar da kasashen Afirka sun bambanta, amma za a iya kaiwa ga cimma buri guda daya. Saboda haka, ci gaban kasar Sin ya karfafa gwiwar jama’ar kasashen Afirka. Mu ma muna son tabbatar da zamanantarwa bisa dogaro da karfin kanmu.”

Ban da haka, Charles Onunaiju, darektan cibiyar nazarin kasar Sin ta kasar Najeriya, ya taba bayyana cewa, babbar matsala da kasashen Afirka suke fama da ita, ita ce talauci. Kana babban dalilin da ya sa muke kokarin zamanantar da kanmu shi ne don biyan bukatun jama’a. A cewarsa, “ Ya kamata mu koyi dabarun da kasar Sin ta samu, a kokarinta na raya kai. Sa’an nan mu yi kokarin ganowa da daidaita muhimmin bangare dake bukatar a daidaita shi, yayin da muke neman raya tattalin arziki da zaman al’umma na kasashen Afirka. ”

Ta jawabansu za mu iya ganin cewa, jami’ai da masana na kasashen Afirka, sun fara dora karin muhimmanci kan kasancewar mabambantan wayewar kai tare (maimakon samun takara da rikici a tsakaninsu), da dogaro da kai a kokarin neman ci gaban kasa ( maimakon rungumar wai “daidaitaccen tsari” na kasashen yamma na tabbatar da ci gaba), da kokarin biyan bukatun jama’a (maimakon dora nauyi kan tsarin kasuwa mai ‘yanci), da sauran tunani, wadanda suka sha bamban da ra’ayoyin kasar Amurka, da na sauran kasashen yammacin duniya.

 

Hakan ba wani abun ban mamaki ba ne, saboda fasahohin da kasar Sin ta samu a kokarin raya kanta, sun nuna mana cewa, dole ne a samu tunani na kai, kafin a kai ga samun cikakken ‘yancin kai. Kana ya kamata a bi hanyar raya kasa ta musamman, da ta dace da yanayin da kasa ke ciki, har a kai ga samar da hakikanin ci gabanta. (Bello Wang)

Tunani
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Hadin Gwiwar BRICS Na Jagorantar Hadin Kan Kasashe Masu Tasowa Da Dogaro Da Karfin Kansu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Shirin Fadada Samar Da Hidimomin Reno Da Na Kiwon Lafiyar Yara Masu Rahusa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gudummawar Da Hada-Hadar Ba Da Hidima Ta Sin Take Kawo Wa Duniya

MASU ALAKA

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka
Ra'ayi Riga

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

September 14, 2026
Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Next Post
Jirgin Sojoji Ɗauki Ya Kai Ba Luguden Wuta A Chikun Ba – Gwamnatin Kaduna

NAF Ta Kashe 'Yan Ta'adda Tare Da Tarwatsa Sansanoninsu A Zamfara 

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

September 15, 2026
Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta

Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta

September 15, 2026
’Yan Ta’adda Sun Kai Wa Ƙauyuka 2 Hari A Adamawa

Boko Haram Sun Kashe Mutane 4 Tare Da Ƙone Gidaje A Adamawa

September 15, 2026
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

September 15, 2026
Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

September 15, 2026
Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

September 15, 2026
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Arziƙin Dangote Ya Haura Dala Biliyan 50 Bayan Fara Sayar Da Hannun Jarin Matatarsa – Forbes

September 15, 2026
Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

September 14, 2026
Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

September 14, 2026
Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

September 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.