‘Yan bindiga sun sace wasu dalibai mata biyu na Jami’ar Al-Qalam da ke Jihar Katsina.
Wadanda lamarin ya rutsa da su, su ne Habiba Ango Shantali da Maryam Abubakar Musa.
- Almundahana: An Gano Karin Biliyan 3 Da Ta Sake Batan Dabo Karkashin Betta Edu
- Mutane Kalilan Ne Suka Sace Dukiyar Nijeriya Ta Hanyar Tallafin Mai – Tinubu
Lamarin ya faru ne yayin da daliban ke kan hanyar komawa makarantar a ranar Litinin, 15 ga watan Janairu, 2024.
Shugaban Kungiyar Daliban Jihar Neja (NANISS) na kasa, Kwamared Gambo Idris Shehu, ya tabbatar da sace daliban a wata sanarwa da sakatare-janar na kungiyar, Kwamared Mohammed Ibrahim ya fitar.
Sanarwar ta kara da cewa, “Mun samu labarin sace wasu dalibanmu biyu na Jihar Neja da ke karatu a Jami’ar Al-Qalam a Jibar Katsina a kan hanyarsu ta komawa makaranta.
“Daliban da aka sace su ne Habiba Ango Shantali da Maryam Abubakar Musa,” in ji sanarwar.
“Muna rokon Allah Ya kubutar da su daga hannun wadanda suka sace su.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp