• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Shimfida Wa Al’ummar Yankin Birnin Gwari Sharudda Noma A Daminan Bana

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohuwa Mai Shekara 120 A Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da dosowar daminar bana, manoma a yankunan Birnin Gwari sun ce har yanzu sharar gona don shirin fara noma ya gagara saboda ‘yan bindiga da ke yankin sun shinfida sharudan da manoman ba za su iya cikawa ba.

Babban dajin Birnin Gwari da ya hada yankunan jihohi uku na Kaduna, Neja da Zamfara, yana daga cikin wuraren da ake noma kaso mafi tsoka na kayan abinci a yankin.

  • Zargin Daukar Nauyin Ta’addanci: Kotu Ta Hana Belin Tukur Mamu

To sai dai tsawon shekaru ke nan manoma a yankin ba sa samun sukunin yin noma, sakamakon mamayar da ‘yan bindiga suka yi a wajen.

Hasali ma kauyuka da dama sun tashi daga yankin, saboda ayyukan ‘yan bindigar, da suka hada da kai hare-hare, satar shanu da kuma satar mutane domin karbar kudin fansa, wanda ya zama ruwan dare a yankin.

Yanzu haka ana tunkarar saukar damina, amma babu alamun wani shirye-shiryen soma kintsawa aikin gona a yankunan na dajin Birnin Gwari da kewaye kamar yadda aka al’adanta, na share gona, kai taki da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Mai sharhi kan lamurran yau da kullum kuma Dan-masanin Birnin Gwari, Alhaji Zubairu Idris Abdurra’uf ya ce bana ma dai lamarin ya ta’azzara, saboda sharudda masu tsaurin gaske da ‘yan bindigar su ka shinfidawa manoma.

Ya ce ”yanzu dai aikin gona ya gagara a yankin Birnin Gwari duk kuwa da bukatar da manoman ke da ita na zuwa gona don soma shirye-shirye da hako arzikin albarkatun noma a yankin.

Wannan matsala dai ta dade tana ci wa mahukuntan Nijeriya tuwo a kwarya, kamar yadda kwamishinan tsaro na Jihar Kaduna Samuel Aruwan ya bayyana wa manema labarai, bayan tashi daga wani taro kan sha’anin tsaro a Kaduna, inda ya ce duk da nasarorin da jami’an tsaro ke samu kan ‘yan bindiga, har yanzu akwai kalubalen tsaro.
To sai dai duk da ta’azzarar wannan matsalar ta tsaro, Dan masanin Birnin Gwari, na ganin akwai mafita idan aka sauya salo.

Ya ce “sai an yi da gaske. Jami’an tsaro suna iya kokarinsu. Amma maganar nan da nake da kai, tsakanin Manina da Mariga ‘yan bindiga na cin karensu ba babbaka. Kullum suna harbe na harbewa, su raunata wasu, sannan su kwashi wasu mutane a shiga da su daji domin karbar kudin fansa.”

“Saboda haka dole jami’an tsaro su sauya salo kuma su kara kaimi, sannan a sami wadanda za su taimaka musu a shiga cikin wadannan dazukan, domin duk abin da aka yi kan hanya idan ba’a shiga dazukan ba, to ba yadda za’a yi a kawo karshen wannan matsala.”

Wannan dai ba shi ne karon farko da ‘yan-bindiga ke shinfida wa manoma sharudan zuwa gonakin su ba, sai dai kuma manazarta na ganin saka ka’idojin tun kafin sharar gona alama ce ta sauya salon da ke bukatar mahukunta su dauki mataki tun kafin abin ya gagari kundila.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Yan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Makafi 88 Sun Zana Jarabawar JAMB A Kano

Next Post

Shin Ana Da Bukatar Tsarin Takaita Zirga-zirgar Kudi A Hannun ‘Yan Nijeriya?

Related

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

58 minutes ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

1 hour ago
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano
Labarai

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

2 hours ago
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

5 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

6 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

18 hours ago
Next Post
Shin Ana Da Bukatar Tsarin Takaita Zirga-zirgar Kudi A Hannun ‘Yan Nijeriya?

Shin Ana Da Bukatar Tsarin Takaita Zirga-zirgar Kudi A Hannun 'Yan Nijeriya?

LABARAI MASU NASABA

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.