• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Shimfida Wa Al’ummar Yankin Birnin Gwari Sharudda Noma A Daminan Bana

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohuwa Mai Shekara 120 A Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da dosowar daminar bana, manoma a yankunan Birnin Gwari sun ce har yanzu sharar gona don shirin fara noma ya gagara saboda ‘yan bindiga da ke yankin sun shinfida sharudan da manoman ba za su iya cikawa ba.

Babban dajin Birnin Gwari da ya hada yankunan jihohi uku na Kaduna, Neja da Zamfara, yana daga cikin wuraren da ake noma kaso mafi tsoka na kayan abinci a yankin.

  • Zargin Daukar Nauyin Ta’addanci: Kotu Ta Hana Belin Tukur Mamu

To sai dai tsawon shekaru ke nan manoma a yankin ba sa samun sukunin yin noma, sakamakon mamayar da ‘yan bindiga suka yi a wajen.

Hasali ma kauyuka da dama sun tashi daga yankin, saboda ayyukan ‘yan bindigar, da suka hada da kai hare-hare, satar shanu da kuma satar mutane domin karbar kudin fansa, wanda ya zama ruwan dare a yankin.

Yanzu haka ana tunkarar saukar damina, amma babu alamun wani shirye-shiryen soma kintsawa aikin gona a yankunan na dajin Birnin Gwari da kewaye kamar yadda aka al’adanta, na share gona, kai taki da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

Mai sharhi kan lamurran yau da kullum kuma Dan-masanin Birnin Gwari, Alhaji Zubairu Idris Abdurra’uf ya ce bana ma dai lamarin ya ta’azzara, saboda sharudda masu tsaurin gaske da ‘yan bindigar su ka shinfidawa manoma.

Ya ce ”yanzu dai aikin gona ya gagara a yankin Birnin Gwari duk kuwa da bukatar da manoman ke da ita na zuwa gona don soma shirye-shirye da hako arzikin albarkatun noma a yankin.

Wannan matsala dai ta dade tana ci wa mahukuntan Nijeriya tuwo a kwarya, kamar yadda kwamishinan tsaro na Jihar Kaduna Samuel Aruwan ya bayyana wa manema labarai, bayan tashi daga wani taro kan sha’anin tsaro a Kaduna, inda ya ce duk da nasarorin da jami’an tsaro ke samu kan ‘yan bindiga, har yanzu akwai kalubalen tsaro.
To sai dai duk da ta’azzarar wannan matsalar ta tsaro, Dan masanin Birnin Gwari, na ganin akwai mafita idan aka sauya salo.

Ya ce “sai an yi da gaske. Jami’an tsaro suna iya kokarinsu. Amma maganar nan da nake da kai, tsakanin Manina da Mariga ‘yan bindiga na cin karensu ba babbaka. Kullum suna harbe na harbewa, su raunata wasu, sannan su kwashi wasu mutane a shiga da su daji domin karbar kudin fansa.”

“Saboda haka dole jami’an tsaro su sauya salo kuma su kara kaimi, sannan a sami wadanda za su taimaka musu a shiga cikin wadannan dazukan, domin duk abin da aka yi kan hanya idan ba’a shiga dazukan ba, to ba yadda za’a yi a kawo karshen wannan matsala.”

Wannan dai ba shi ne karon farko da ‘yan-bindiga ke shinfida wa manoma sharudan zuwa gonakin su ba, sai dai kuma manazarta na ganin saka ka’idojin tun kafin sharar gona alama ce ta sauya salon da ke bukatar mahukunta su dauki mataki tun kafin abin ya gagari kundila.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Yan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Makafi 88 Sun Zana Jarabawar JAMB A Kano

Next Post

Shin Ana Da Bukatar Tsarin Takaita Zirga-zirgar Kudi A Hannun ‘Yan Nijeriya?

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

10 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

10 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

11 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

12 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

12 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

13 hours ago
Next Post
Shin Ana Da Bukatar Tsarin Takaita Zirga-zirgar Kudi A Hannun ‘Yan Nijeriya?

Shin Ana Da Bukatar Tsarin Takaita Zirga-zirgar Kudi A Hannun 'Yan Nijeriya?

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.