• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Yi Sanadin Tashin Farashin Kayan Abinci A Taraba

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kayan abinci sun yi tashin gwauron zabi a Jihar Taraba, biyo bayan yadda ayyukan ‘yan bindiga ya yi kamari a jihar, wanda hakan ya hana manoma girbe amfanin gonakinsu da suka noma a bana.

Bincike ya nuna cewa, ‘yan bindigar sun hana manoma shiga cikin gonakinsu, don girbe abin da suka shuka a Kananan Hukumomin Bali, Ussa, Takum da kuma Ardo Kola da ke jihar.

Don haka, yanzu farashin buhun masara mai nauyin kilo 100, ana sayar da shi kan naira 32,000, sabanin yadda ake sayar da shi a shekarar da ta wuce kan naira 18,000.

Bugu da kari, farashin buhun shinkafar gida, ana sayar da mai nauyin kilo 100 kan naira 25,000, sabanin yadda ake sayarwa a shekarar da ta gabata kan naira 17,000.

Har ila yau, ‘yan bindigar sun hallaka manoma da dama tare da yin garkuwa da manoma da yawa a fadin wadannan kananan hukumomi.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Wata manomiya mai suna Lami John ta bayyana cewa, ‘yan bindigar sun hana su girbe amfanin gonakinsu a yankin Kwando na Karamar Hukumar Ardo Kola.
Sannan ta sanar da cewa, ‘yan bindigar sun yi sace manoma da dama; ciki har da ita kanta da kuma ‘ya’yanta, amma wasu suka samu nasarar har da ita da kuma ‘ya’yan nata daga dajin da aka kai su.

Bugu da kari, a Kananan Hukumomin Ussa da Takum, an kashe manoma da dama a wasu hare-haren da ‘yan bindigar suka kai a kwanakin baya tare da hallaka manoma da dama, wanda hakan ya jawo manoman suka gaza girbe amafnin da suka noma a gonakin nasu.

Wani manomi mai suna Mista Bulus Andeyake ya bayyana cewa, ‘yan bindigar sun kutsa a cikin yankunan nasu, inda hakan ya sa manoma a yankunan su gaza girbe amfanin gonar da suka noma.
Ya ci gaba da cewa, suna sayar da rayukansu ne idan za su tafi gona, domin a ko’ina akwai ‘yan bindigar da ke firgita manoman.

Bulus ya kara da cewa, ‘yan bindigar a ‘yan watannin baya sun sake hallaka wasu manoma goma sha daya a yankin Jenuwagida a lokacin da suke kan girbe amfanin gonarsu.
Kazalika ya sanar da cewa, ‘yan bindigar sun kuma kashe wasu manoma biyu a yankin Jenuwagida a cikin gonakinsu a makon da ya wuce.

Andeyake ya yi kira ga jami’an tsaro da su kara kokari wajen yakar wadannan ‘yan bindiga, domin gonakan manoman a yankunan su kubuta.

Shi ma wani takwaransa mai suna Dauda Maihula ya bayyana cewa, manoma da dama na jin tsoron zuwa gonakinsu, domin girbe amfanin gona, sakamakon yadda ‘yan bindigar suka mamaye gonakin nasu.
A cewar tasa, ‘yan bindigar sun kuma kashe mafarauta da dama a wata fafatawa da suka yi da su a makon da ya gabata.

Bugu da kari, wani mai sana’ar sayar da hatsi a kasuwar sayar da hatsi ta Iware, Alhaji Haruna Jafar ya bayyana cewa, farashin kayan abincin zai ci gaba da tashi sakamakon wannan aiki na ‘yan bindiga a wadannan yankuna.
Ya ci gaba da cewa, a yankin Kwando da ke Karamar Hukumar Ardo Kola da kuma yankin Dakka a Karamar Hukumar Bali, ‘yan bindigar sun karbe yankuna da dama wanda manoman ke zaune.

Haka zalika ya sanar da cewa, hakan ya jawo hana manoman yankunan girbe amfanin gonakinsu da suka noma.
Ya kara da cewa, manoma da dama da suka noma shinkafa, masara, waken soya da farin wake, sun gaza girbe amfanin sakamakon wadannan hare-hare na ‘yan bindiga.

Kazalika, a karshe ya kuma yaba wa mafarauta da sauran jami’an tsaro, kan kokarin da suke yi na yakar wadannan ‘yan bindiga a yankunan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: TarabaYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Ya Gana Da Manyan Jami’an Saudiyya Da Iran

Next Post

Yaudarar Samari Kan Aure Bayan Budurwa Ta Lume A Soyayya

Related

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

7 days ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

7 days ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

2 weeks ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

2 weeks ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

3 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

4 weeks ago
Next Post
Yaudarar Samari Kan Aure Bayan Budurwa Ta Lume A Soyayya

Yaudarar Samari Kan Aure Bayan Budurwa Ta Lume A Soyayya

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.