ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Yi Sanadin Tashin Farashin Kayan Abinci A Taraba

by Abubakar Abba
3 years ago
Abinci

Kayan abinci sun yi tashin gwauron zabi a Jihar Taraba, biyo bayan yadda ayyukan ‘yan bindiga ya yi kamari a jihar, wanda hakan ya hana manoma girbe amfanin gonakinsu da suka noma a bana.

Bincike ya nuna cewa, ‘yan bindigar sun hana manoma shiga cikin gonakinsu, don girbe abin da suka shuka a Kananan Hukumomin Bali, Ussa, Takum da kuma Ardo Kola da ke jihar.

Don haka, yanzu farashin buhun masara mai nauyin kilo 100, ana sayar da shi kan naira 32,000, sabanin yadda ake sayar da shi a shekarar da ta wuce kan naira 18,000.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, farashin buhun shinkafar gida, ana sayar da mai nauyin kilo 100 kan naira 25,000, sabanin yadda ake sayarwa a shekarar da ta gabata kan naira 17,000.

Har ila yau, ‘yan bindigar sun hallaka manoma da dama tare da yin garkuwa da manoma da yawa a fadin wadannan kananan hukumomi.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Wata manomiya mai suna Lami John ta bayyana cewa, ‘yan bindigar sun hana su girbe amfanin gonakinsu a yankin Kwando na Karamar Hukumar Ardo Kola.
Sannan ta sanar da cewa, ‘yan bindigar sun yi sace manoma da dama; ciki har da ita kanta da kuma ‘ya’yanta, amma wasu suka samu nasarar har da ita da kuma ‘ya’yan nata daga dajin da aka kai su.

Bugu da kari, a Kananan Hukumomin Ussa da Takum, an kashe manoma da dama a wasu hare-haren da ‘yan bindigar suka kai a kwanakin baya tare da hallaka manoma da dama, wanda hakan ya jawo manoman suka gaza girbe amafnin da suka noma a gonakin nasu.

Wani manomi mai suna Mista Bulus Andeyake ya bayyana cewa, ‘yan bindigar sun kutsa a cikin yankunan nasu, inda hakan ya sa manoma a yankunan su gaza girbe amfanin gonar da suka noma.
Ya ci gaba da cewa, suna sayar da rayukansu ne idan za su tafi gona, domin a ko’ina akwai ‘yan bindigar da ke firgita manoman.

Bulus ya kara da cewa, ‘yan bindigar a ‘yan watannin baya sun sake hallaka wasu manoma goma sha daya a yankin Jenuwagida a lokacin da suke kan girbe amfanin gonarsu.
Kazalika ya sanar da cewa, ‘yan bindigar sun kuma kashe wasu manoma biyu a yankin Jenuwagida a cikin gonakinsu a makon da ya wuce.

Andeyake ya yi kira ga jami’an tsaro da su kara kokari wajen yakar wadannan ‘yan bindiga, domin gonakan manoman a yankunan su kubuta.

Shi ma wani takwaransa mai suna Dauda Maihula ya bayyana cewa, manoma da dama na jin tsoron zuwa gonakinsu, domin girbe amfanin gona, sakamakon yadda ‘yan bindigar suka mamaye gonakin nasu.
A cewar tasa, ‘yan bindigar sun kuma kashe mafarauta da dama a wata fafatawa da suka yi da su a makon da ya gabata.

Bugu da kari, wani mai sana’ar sayar da hatsi a kasuwar sayar da hatsi ta Iware, Alhaji Haruna Jafar ya bayyana cewa, farashin kayan abincin zai ci gaba da tashi sakamakon wannan aiki na ‘yan bindiga a wadannan yankuna.
Ya ci gaba da cewa, a yankin Kwando da ke Karamar Hukumar Ardo Kola da kuma yankin Dakka a Karamar Hukumar Bali, ‘yan bindigar sun karbe yankuna da dama wanda manoman ke zaune.

Haka zalika ya sanar da cewa, hakan ya jawo hana manoman yankunan girbe amfanin gonakinsu da suka noma.
Ya kara da cewa, manoma da dama da suka noma shinkafa, masara, waken soya da farin wake, sun gaza girbe amfanin sakamakon wadannan hare-hare na ‘yan bindiga.

Kazalika, a karshe ya kuma yaba wa mafarauta da sauran jami’an tsaro, kan kokarin da suke yi na yakar wadannan ‘yan bindiga a yankunan.

Abinci
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Yaudarar Samari Kan Aure Bayan Budurwa Ta Lume A Soyayya

Yaudarar Samari Kan Aure Bayan Budurwa Ta Lume A Soyayya

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.