ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Yi Sanadin Tashin Farashin Kayan Abinci A Taraba

by Abubakar Abba
3 years ago
Abinci

Kayan abinci sun yi tashin gwauron zabi a Jihar Taraba, biyo bayan yadda ayyukan ‘yan bindiga ya yi kamari a jihar, wanda hakan ya hana manoma girbe amfanin gonakinsu da suka noma a bana.

Bincike ya nuna cewa, ‘yan bindigar sun hana manoma shiga cikin gonakinsu, don girbe abin da suka shuka a Kananan Hukumomin Bali, Ussa, Takum da kuma Ardo Kola da ke jihar.

Don haka, yanzu farashin buhun masara mai nauyin kilo 100, ana sayar da shi kan naira 32,000, sabanin yadda ake sayar da shi a shekarar da ta wuce kan naira 18,000.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, farashin buhun shinkafar gida, ana sayar da mai nauyin kilo 100 kan naira 25,000, sabanin yadda ake sayarwa a shekarar da ta gabata kan naira 17,000.

Har ila yau, ‘yan bindigar sun hallaka manoma da dama tare da yin garkuwa da manoma da yawa a fadin wadannan kananan hukumomi.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Wata manomiya mai suna Lami John ta bayyana cewa, ‘yan bindigar sun hana su girbe amfanin gonakinsu a yankin Kwando na Karamar Hukumar Ardo Kola.
Sannan ta sanar da cewa, ‘yan bindigar sun yi sace manoma da dama; ciki har da ita kanta da kuma ‘ya’yanta, amma wasu suka samu nasarar har da ita da kuma ‘ya’yan nata daga dajin da aka kai su.

Bugu da kari, a Kananan Hukumomin Ussa da Takum, an kashe manoma da dama a wasu hare-haren da ‘yan bindigar suka kai a kwanakin baya tare da hallaka manoma da dama, wanda hakan ya jawo manoman suka gaza girbe amafnin da suka noma a gonakin nasu.

Wani manomi mai suna Mista Bulus Andeyake ya bayyana cewa, ‘yan bindigar sun kutsa a cikin yankunan nasu, inda hakan ya sa manoma a yankunan su gaza girbe amfanin gonar da suka noma.
Ya ci gaba da cewa, suna sayar da rayukansu ne idan za su tafi gona, domin a ko’ina akwai ‘yan bindigar da ke firgita manoman.

Bulus ya kara da cewa, ‘yan bindigar a ‘yan watannin baya sun sake hallaka wasu manoma goma sha daya a yankin Jenuwagida a lokacin da suke kan girbe amfanin gonarsu.
Kazalika ya sanar da cewa, ‘yan bindigar sun kuma kashe wasu manoma biyu a yankin Jenuwagida a cikin gonakinsu a makon da ya wuce.

Andeyake ya yi kira ga jami’an tsaro da su kara kokari wajen yakar wadannan ‘yan bindiga, domin gonakan manoman a yankunan su kubuta.

Shi ma wani takwaransa mai suna Dauda Maihula ya bayyana cewa, manoma da dama na jin tsoron zuwa gonakinsu, domin girbe amfanin gona, sakamakon yadda ‘yan bindigar suka mamaye gonakin nasu.
A cewar tasa, ‘yan bindigar sun kuma kashe mafarauta da dama a wata fafatawa da suka yi da su a makon da ya gabata.

Bugu da kari, wani mai sana’ar sayar da hatsi a kasuwar sayar da hatsi ta Iware, Alhaji Haruna Jafar ya bayyana cewa, farashin kayan abincin zai ci gaba da tashi sakamakon wannan aiki na ‘yan bindiga a wadannan yankuna.
Ya ci gaba da cewa, a yankin Kwando da ke Karamar Hukumar Ardo Kola da kuma yankin Dakka a Karamar Hukumar Bali, ‘yan bindigar sun karbe yankuna da dama wanda manoman ke zaune.

Haka zalika ya sanar da cewa, hakan ya jawo hana manoman yankunan girbe amfanin gonakinsu da suka noma.
Ya kara da cewa, manoma da dama da suka noma shinkafa, masara, waken soya da farin wake, sun gaza girbe amfanin sakamakon wadannan hare-hare na ‘yan bindiga.

Kazalika, a karshe ya kuma yaba wa mafarauta da sauran jami’an tsaro, kan kokarin da suke yi na yakar wadannan ‘yan bindiga a yankunan.

Abinci
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Yaudarar Samari Kan Aure Bayan Budurwa Ta Lume A Soyayya

Yaudarar Samari Kan Aure Bayan Budurwa Ta Lume A Soyayya

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.