• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Yi Yunkurin Mamaye Garin Safana Da Raunata ‘Yan Sanda 2 – Yan Sanda

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
'Yan bindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta tabbatar da wani hari da ‘yan bindiga suka kai a garin Safana inda suka raunata mutane uku, mutum biyu daga cikin jami’an tsaro.

Kakakin rundunar ‘yansanda na jihar Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu, ne ya tabbatar da haka ga wakilin LEADERSHIP HAUSA a Katsina.

  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Za Ta Fara Bai Wa Malamai Da Masu Unguwanni Alawus
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Ta Kaddamar Da Matasa ‘Yan Sa-Kai

Aliyu, ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun so mamaye garin na Safana a cikin dare da misalin karfe 6:00 na maraice inda suka zo ne da muggan makamai suka fara harbi kan mai uwa da wabi.

Sai dai a cewar sa, baturen ‘yan sanda na Safana ya shirya wata tawaga ta jami’an tsaro inda suka fatataki ‘yan bindigar daga garin Safana.

“A lokacin wannan ɗauki ba daɗi da ‘yan bindiga sun raunata jami’anmu guda biyu tare da wani mutum ɗaya wanda yanzu haka suna asibiti ana ba su kulawa ta musamman ‘ inji shi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Ya ƙara da cewa tuni jami’ansu, suka bazama domin kamo waɗanda suka kai wannan hari. Kuma tuni an fara bincike a kan lamarin.

A nasa ɓangaren, ɗan majalisar dokokin jihar Katsina mai wakiltar ƙaramar hukumar Safana wanda shi ne mataimakin kakakin majalisar Hon. Abduljalal Haruna Runka, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Honarabul Abduljalal Runka wanda ya ce ya zuwa yanzu komai ya lafa, sai dai ya tabbatar da cewa jami’an tsaro sun halaka ‘ yan bindiga da dama wanda sai nan gaba za a ji yawansu.

” Yanzu nan maganar da nake da kai, mun samu labarin cewa an yi wa ɓarayin daji ɓarna sosai, kuma hakan ya faru ne saboda jajircewar jami’an tsaro da kuma dakarun tsaro na ‘Community Watch Corps’

A cewarsa, babu labarin kashe ko mutum ɗaya, sannan ba su yi nasarar sace kowa ba, sai dai sun kutsa kai cikin wani shagon sayar da magunguna sun kwashe masa ciniki.

Kamar yadda Honarabul Abduljalal Runka ya tabbatarwa manema labarai, ya ce, ‘yan bindigar sun zo ne a kan mashina akalla talatin, amma a cikin ikon Allah jami’an tsaro sun fatatake su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Asuu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro
Labarai

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
majalisar kasa
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
Next Post
Wasu Mazauna Abuja Sun Shiga Rumbun Ajiya Na Hukumar NEMA Sun Sace Kayan Abinci

Wasu Mazauna Abuja Sun Shiga Rumbun Ajiya Na Hukumar NEMA Sun Sace Kayan Abinci

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.