ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Za Ta Fara Bai Wa Malamai Da Masu Unguwanni Alawus

by Sadiq
3 years ago
Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce za ta fara bai wa malaman Masallatan Juma’a da mataimakansu da masu unguwanni alawus-alawus domin karfafa musu gwiwa wajen yaki da rashin tsaro.

Gwamna Dikko Radda ne ya bayyana hakan bayan kaddamar da kwamitocin gudanarwa na kungiyar Katsina Community Watch Corps (KCSWC).

  • NFF Ta Sanar Da Ranar Fara Gasar ‘Federation Cup’ Ta Nijeriya
  • Gwamnan Zamfara Zai Binciki Badakalar Miliyan 774 A Hukumar Alhazai Ta Jihar

A wata sanarwa da babban sakataren yada labaransa, Ibrahim Kaula-Mohammed ya fitar, ya ruwaito Radda na cewa kwamitin zai hada kai da sauran jami’an tsaro wajen zakulo ‘yan bindiga a fadin jihar.

ADVERTISEMENT

Ya ce mambobin kwamitin gudanarwa na kowace karamar hukuma 34 sun hada da kansila, hakimin gunduma, jami’in ‘yansanda na shiyya da wakilan hukumomin tsaro daban-daban.

Sannan ya ce akwai wakilai biyu na ‘yan kasuwa da kuma wakilan kungiyoyin addini.

LABARAI MASU NASABA

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Gwamnan ya ce kwamitin zai sa ido tare da tantance ayyukan KCSWC a yankunansu tare da gabatar da rahoton wata-wata ga kwamishinan tsaron cikin gida na jihar.

Tun da fari, kwamishinan tsaron cikin gida na jihar, Dakta Nasiru Mu’azu-Danmusa, ya bayyana cewa sannu a hankali rashin tsaro na raguwa a fadin jihar tun da aka kafa KCSWC.

A nasu jawabin wakilan mai martaba Sarkin Katsina, Alhaji Aminu Nuhu Abdulkadir da mai shari’a Saddik Abdullahi Mahuta (mai ritaya), sun yaba wa gwamnan bisa daukar matakan magance matsalar rashin tsaro a jihar.

Abdulkadir, wanda shi ne hakimin Rimi da Abdullahi Mahuta, hakimin Malumfashi, sun yi alkawarin ci gaba da bai wa kwamitin goyon baya.

MASU ALAKA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Next Post
Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Karawa Juna Sani Na Kasa Da Kasa Game Da Diflomasiyyar Kasar Sin

Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Karawa Juna Sani Na Kasa Da Kasa Game Da Diflomasiyyar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Katsina

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Katsina

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.