• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya 376 Aka Kwaso Daga Sudan – Minista Sadiya

Ba za mu bar ko mutum ɗaya a ƙasar ba, inji ta

by Sulaiman
2 years ago
Minista Sadiya

Jimillar ‘yan Nijeriya 376 da su ka maƙale a ƙasar Sudan sun iso Abuja lafiya sakamakon aikin kwaso su da Gwamnatin Tarayya ke yi. 

 

Mai ba da shawara ga Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Miss Nneka Anibeze, ita ce ta bayyana haka a wata sanarwa da ta ba manema labarai a ranar Alhamis.

  • Shekara 61 Da Haihuwar Sam Nda-Isaiah: Waiwayen Mukarrabai Kan Mashahuran Hikimominsa

Ta ƙara da cewa kashin farko na mutanen da aka kwaso, wato mutum 94, sun sauka ne a daren ranar Laraba a jirgin Rundunar Mayaƙan Sama na Nijeriya samfurin Hercules C-130, yayin da sauran mutum 282 su ka sauka a jirgin kamfanin Air Peace.

 

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ita ce ta tsaya a filin jirgin sama na Abuja domin tarbar waɗanda aka ceto daga Sudan ɗin.

 

A jawabin maraba da ta yi masu, ministar ta yi godiya ga Gwamnatin Tarayya saboda tattaunawar fahimtar juna da ta yi da gwamnatin Sudan wadda har ta kai ga samun karɓar ‘yan Nijeriya tare da kwaso su daga ƙasar da yaƙi ya ɓarke.

Minista Sadiya

Ta ce: “Mun yi murna da ganin sun iso lafiya kuma babu wani rai da ya salwanta. Sun sha matuƙar wahala amma mun gode wa Allah da su ka iso gida lafiya.

 

“Mu na gode wa Gwamnatin Tarayya saboda nasarar da aka samu a aikin ceto ‘yan Nijeriyar da ke Sudan. Mu na addu’ar a samu zaman lafiya a Sudan da ma kowane ɓangare na ƙasar nan.

 

“Yaƙi ba abu ne mai kyau ba. Kun dai ga yadda mutanen da su ka tafi karatu su ka zama ‘yan gudun hijira ba zato ba tsammani. Wannan ba kawai bala’i ne na ƙasa da ƙasa ba, a’a, bala’i ne kuma da ya shafi jinƙan rayuwar bil’adama.

 

“Za mu ba ko wannen su kuɗi N100,000 domin su yi kuɗin mota zuwa wajen iyalan su. Haka kuma mun tanadar da masauki a otal ga waɗanda aka kwaso ɗin har sai sun haɗu da iyalan su, yayin da kuma waɗanda ke buƙatar a duba lafiyar su an yi masu hakan.“

 

Minista Sadiya kuma ta bayyana cewa kamar yadda Shugaba Muhammadu Buhari ya umarta, babu wani ɗan Nijeriya da ke son ya tsere daga halin da ake ciki a Sudan da za a bar shi a baya.

 

Ta ce, “Ma’aikatar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa da kuma Ma’aikatar Harkokin Ƙasashen Waje da sauran ma’aikatun gwamnati irin su NEMA, NCFRMI, NIDCOM, NIA da Rundunar Mayaƙan Sama na Nijeriya su na aiki tare da Ofisoshin Jakadancin Nijeriya da ke Sudan, Masar, Etofiya da Chadi domin tabbatar da cewa ko mutum ɗaya ba a baro ba. Don haka, dukkan ɗan Nijeriyar da ke so ya tsere daga halin da ake ciki a Sudan za a dawo da shi gida cikin tsaro da darajtawa.

 

“Aikin kwashe mutanen ya gudana ne ta hanyoyi masu wuyar sha’ani na wasu mutane da su ka zama dillalai a lamarin, wanda hakan ne ya sa aka riƙa fuskantar matsalolin da aikin ya ci karo da su. An shirya ci gaba da kwaso mutanen mu kuma aikin zai gudana da sauri-sauri fiye da da har sai an kwashe dukkan ‘yan Nijeriya da ke Sudan an kawo su gida.”

 

Ita dai Sudan, ta auka cikin rikicin yaƙi ne a ranar 15 ga Afrilu lokacin da wasu sassa na sojojin ƙasar masu adawa da juna su ka fara kai wa juna hari a birnin Khartoum da yankin Darfur.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Next Post
A Nijeriya Ake Sarrafa Taliyar Indomie, Ana iya Amfani Da Ita Ba Matsala – Shugabar NAFDAC

A Nijeriya Ake Sarrafa Taliyar Indomie, Ana iya Amfani Da Ita Ba Matsala – Shugabar NAFDAC

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.