• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Na Dandana Kudarsu A Mulkin Tinubu — PDP

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa ‘yan Nijeriya na dandana kula luransu a karkashin jagorancin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC.

A wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba ya fitar a ranar Litinin da ta gabata, cewa babbar jam’iyyar adawar ta koka kan yadda Nijeriya ta shiga tsaka mai wuya a karkashin jam’iyyar APC da Tinubu yake jagoranta, wadda ba ta damu da ‘yan kasa ba, al’amarin da ya haifar da yanayi na rashin nagartaccen shugabanci a kasar nan.

  • Ba Za Mu Sake Lamuntar Kumbiya-kumbiyar Da Ake Tafkawa Wurin Fasfo Ba – Ministan Cikin Gida
  • Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Tallafawa Mali Bayan Janyewar Dakarun MINUSMA

Sanarwar ta kara da cewa, “Jam’iyyar ta firgita da yadda aka samu rashin jituwa mai tsanani tsakanin gwamnati da ‘yan kasa sakamakon rashin tsari da kuma gaggawar aiwatar da manufofin da suka kawo wahalhalu mai tsanani, rashin tsaro da kuma fargabar da tuni ke barazana ga zaman lafiyar al’umma da hadin kai da wanzuwar kasar nan.

“Rashin wayo ne da sanin ya kamata da gwamnati ta yi wajen cire tallafin man fetur da karya darajar naira wanda ya janyo tsadar rayuwa da ya gurgunta mana tattalin arzikin kasa, sannan ya durkusar da miliyoyin ‘yan kasuwa tare da jawo asarar ayyuka masu dimbin yawa da karuwar talauci da yunwa da rashin tsaro a fadin kasar nan.

“Lmarin ya janyo mummunar asarar ga masu saka hannun jari tare da ficewar kamfanonin tare da barin miliyoyin ‘yan Nijeriya neman aikin yi da gurgunta masu kanana da matsakaitan masana’antu wadanda su ne ainihin ginshikan tattalin arzikin kasarmu.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

“Abin ban tsoro ne cewa a cikin watanni biyun da suka gabata, sama da ‘yan Nijeriya miliyan 150 ba za su iya ciyar da iyalansu abinci ba, inda suke kwana da yauwa.

“Abin takaici ne yadda gwamnatin APC ke ci gaba da yaudarar ‘yan Nijeriya da bayar da tallafi na raba buhunan shinkafa 1,200 ga mutane a kowace jiha. Jam’iyyar APC ta fadada karfinta na yaudara da damfarar ‘yan Nijeriya ta hanyar shirye-shiryen marasa amfani.”

PDP ta bayyana damuwata game da abin da ta lura akwai rashin tausayi, damuwa da raba kan ‘yan kasa, idan ba a yi gaggawar magance lamarin ba zai iya harfar da mummunan rikici.”

Ta kuma bukaci ‘yan Nijeriya da su kwantar da hankalinsu su kasance masu bin doka da oda da kuma mara wa juna baya a kokarinsu na samar da kasa mai tsaro da ci gaban tattalin arziki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Amfanin Gona Takwas Da Ake Saurin Girbewa Cikin Wata Shida

Amfanin Gona Takwas Da Ake Saurin Girbewa Cikin Wata Shida

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.