• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Na Dandana Kudarsu A Mulkin Tinubu — PDP

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan Nijeriya Na Dandana Kudarsu A Mulkin Tinubu — PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa ‘yan Nijeriya na dandana kula luransu a karkashin jagorancin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC.

A wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba ya fitar a ranar Litinin da ta gabata, cewa babbar jam’iyyar adawar ta koka kan yadda Nijeriya ta shiga tsaka mai wuya a karkashin jam’iyyar APC da Tinubu yake jagoranta, wadda ba ta damu da ‘yan kasa ba, al’amarin da ya haifar da yanayi na rashin nagartaccen shugabanci a kasar nan.

  • Ba Za Mu Sake Lamuntar Kumbiya-kumbiyar Da Ake Tafkawa Wurin Fasfo Ba – Ministan Cikin Gida
  • Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Tallafawa Mali Bayan Janyewar Dakarun MINUSMA

Sanarwar ta kara da cewa, “Jam’iyyar ta firgita da yadda aka samu rashin jituwa mai tsanani tsakanin gwamnati da ‘yan kasa sakamakon rashin tsari da kuma gaggawar aiwatar da manufofin da suka kawo wahalhalu mai tsanani, rashin tsaro da kuma fargabar da tuni ke barazana ga zaman lafiyar al’umma da hadin kai da wanzuwar kasar nan.

“Rashin wayo ne da sanin ya kamata da gwamnati ta yi wajen cire tallafin man fetur da karya darajar naira wanda ya janyo tsadar rayuwa da ya gurgunta mana tattalin arzikin kasa, sannan ya durkusar da miliyoyin ‘yan kasuwa tare da jawo asarar ayyuka masu dimbin yawa da karuwar talauci da yunwa da rashin tsaro a fadin kasar nan.

“Lmarin ya janyo mummunar asarar ga masu saka hannun jari tare da ficewar kamfanonin tare da barin miliyoyin ‘yan Nijeriya neman aikin yi da gurgunta masu kanana da matsakaitan masana’antu wadanda su ne ainihin ginshikan tattalin arzikin kasarmu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

“Abin ban tsoro ne cewa a cikin watanni biyun da suka gabata, sama da ‘yan Nijeriya miliyan 150 ba za su iya ciyar da iyalansu abinci ba, inda suke kwana da yauwa.

“Abin takaici ne yadda gwamnatin APC ke ci gaba da yaudarar ‘yan Nijeriya da bayar da tallafi na raba buhunan shinkafa 1,200 ga mutane a kowace jiha. Jam’iyyar APC ta fadada karfinta na yaudara da damfarar ‘yan Nijeriya ta hanyar shirye-shiryen marasa amfani.”

PDP ta bayyana damuwata game da abin da ta lura akwai rashin tausayi, damuwa da raba kan ‘yan kasa, idan ba a yi gaggawar magance lamarin ba zai iya harfar da mummunan rikici.”

Ta kuma bukaci ‘yan Nijeriya da su kwantar da hankalinsu su kasance masu bin doka da oda da kuma mara wa juna baya a kokarinsu na samar da kasa mai tsaro da ci gaban tattalin arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Tsaron Sin Ta Jaddada Layin Da Bai Dace A Tsallaka Ba A Tattaunawar Soji Tsakanin Sin Da Amurka

Next Post

Amfanin Gona Takwas Da Ake Saurin Girbewa Cikin Wata Shida

Related

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

5 days ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

1 month ago
Next Post
Amfanin Gona Takwas Da Ake Saurin Girbewa Cikin Wata Shida

Amfanin Gona Takwas Da Ake Saurin Girbewa Cikin Wata Shida

LABARAI MASU NASABA

Hukumar kashe gobara

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

June 5, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

June 5, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.