• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Na Kukan Yunwa

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Nijeriya Na Kukan Yunwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin yanzu ‘yan Nijeriya, ba tare da banbancin siyasa, addini ko bangaranci ba suna nuna mamakinsu a kan yadda kasar nan ta samu kanta a wannan hali na tabarbarewar tattalin arziki da tsadar rayuwa. Rayuwa ta yi arha amma abin da rayuwar za ta ci ya yi matukar tashi kamar na gwauron zabo, wannan kuma ya sabawa dukkan ka’idoji na dimokuradiyya wadanda ta yi wa al’umma alkawarin ingantaciyar rayuwa.

Wannan ba kuma yana nufin cewa, Nijeriya ta taba tsallakawa tudun muntsira ba ne, amma abin da ke tayar da hankali shi ne yadda aka yi wa al’umma alkawari tare da shafa masu romon baka amma kuma sai gashi rayuwa ta zama abin da ta zama, al’umma na fama da yunwa a sassan kasa, ‘yan siyasa sun kasa cika alkawuran da suka yi a lokacin da suke yakin neman zabe.

  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta
  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje

Abubuwan da suka faru a jihohin Neja da Kano da wasu wuraren a sassan Nijeriya alamu ne da su ke nuna cewa, nan gaba kadan ‘yan Nijeriya za su fito su nemai a yi masu adalci saboda daga dukkan alamu ‘yan Nijeriya sun fusata. A yayin da al’umma suka yi kumajin fitowa don nunan rashin amincewarsu da matsalolin da ake fama da su na yunwa da tsadar rayuwa wadanda suke ya kama hanyar durkusar da dukkan sassan tattalin arzikin kasa, to lallai alama ce da ya kamata shugabanni su dauka da muhimmanci.

A Kano, masu zanga-zangar ba suna neman a basu wani abu daban ba ne, suna neman a sama masu abubuwan da zai kawo musu saukin rayuwa ne kamar abinci, saukin kudin makaranta da kuma uwa uba a kawo masu saukin matsalar tsaro da ta addabi al’umma ta yadda za su iya barci ba tare da wata fargaba ba. Sun kuma nemi a bude iyakokin kasa ta yadda za a samu shigo da abinci da sauran kayayyaki don taimaka wajen kawo saikin wadanda ake samar wa a cikin gida.

Idan za a iya tunawa an kulle iyakokin kasar nan ne domin dakile yadda ake shigo da kayan abinci saboda yadda manoma suka yi korafin cewa, shigo da kayan abinci yana durkushe kokarin da suke yi na samar da abinci a cikin gida, amma shin wannan mataki na kulle iyakoki za mu iya cewa, kwalliya ta biya kudin sabulu kuwa?

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Matsalolin da rufe iyakokin kasar nan ya haifar yana ci gaba da illata al’umma da kuma mummunar shawarar da aka ba gwamnati ta kara kudaden haraji a akan wasu kayan gona da ake shigowa dasu daga kasashen waje. Gwamnati ta sa burin tattaro kudaden haraji koda kuwa mutane za su rasa rayukansu ne. tabbas wadannan manufofin na gwamnati basu da alfanu ga rayuwar al’umma.

A ra’ayinmu, kamar mutum da aka kai shi bango, alamu yana nuna mutane na yi wa manufofin gwamnati tutsu kamar yadda muka gani a wasu sassan Nijeriya a ‘yan kwanakin nan. Ko ‘yan NIjeiya na nuna cewa, takurawar ya isa haka nan ne? wannan kuma yana nuna cewa, duk wanda aka takura ba wanda ya isa ya san abin da zai iya yi na tawaye a nan gaba.

Matsalolin da kulle iyakokin kasar ta haifar da karin haraji a kan kayan abinci da ake shigowa da sun kara tabarbarewar matsalar staro, abin da ya sa manoma basa iya zuwa gonakinsu haka ma in lokacin girbi ya yi sai sun samu izinin ‘yan ta’adda da kuma yadda aka muhimmantar da dala a sha’anin tattalin arzikin kasar nan duk sun jefa al’umma cikin matsaloli da tsadar rayuwa.

Ga dukkan wadanna matsalolin martanin gamnati mai ci bai wadatar ba, sai wai gashi ana cewa, ‘yan Nijeriya cewa, abinci ya fi arhra fiye da koina a Afirka, tabbas wanna karya ne tsagwaronta, muna bukatar sanin wanda ya yi wannan bincike da kuma wace hujjoji ya yi amfani da ita.

Bayan haka kuma sai ga shi kuma ana neman mayar da matsalar ta zama tamkar siyasa, ana neman a ce, ‘yan Nijeriya sun zama wawayen da har sai da ‘yan adawa ne ke amfanai da su wajen bayyana halin da suke ci na matsin rayuwa, wannan abin takaici ne.

Gaskiya a halin yanzu al’umma na cikin yunwa, ‘yan Njjeriya na fuskantar yunwa da suna kuma cikin haushi kuma akwai rudewa na sanin ainihin anihin abin da ya kamata su yi. Amma kuma rikicin shi ne in har aka samu rudewa da yunwa da kuma fushi abubuwa sun lalace, ya kamata gwamnati a dukkan mataki su dauki matakin yayyafawa al’amarin ruwa don kada al’marin ya zama wani abu daban.

Ya kamata kada ‘yan siyasa su raina al’umma, musamman ganin sune suka kai matakin da suke a halin yanzu, ba wai a ce wa talakawa su yi ta hakuri ba tare da jiran tsammani, in har haka gaskiya ne me ya sa su masu tafiyar da mulki wani irin hakuri suke yi a wajen tafiyar da rayuwar su.?

A ra’ayinmu, ya kamata gwamnati ta fuskanci nauyin da al’umma suka dora musu su kuma fahimci cewa tabbas ana fuskantar yunwa a sassan kasa, mutane na mutuwa saboda rashin abinci. Al’umma na kukan yunwa!!


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Adadin Zirga-zirgar Fasinjoji A Jiragen Kasa Ya Zarce Miliyan 230 A Rabin Farko Na Wa’adin Hutun Bikin Bazara

Next Post

Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa

Related

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

3 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

9 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

12 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

13 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

21 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

1 day ago
Next Post
Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa

Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.