• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Na Kukan Yunwa

by Leadership Hausa
2 years ago
Yunwa

A halin yanzu ‘yan Nijeriya, ba tare da banbancin siyasa, addini ko bangaranci ba suna nuna mamakinsu a kan yadda kasar nan ta samu kanta a wannan hali na tabarbarewar tattalin arziki da tsadar rayuwa. Rayuwa ta yi arha amma abin da rayuwar za ta ci ya yi matukar tashi kamar na gwauron zabo, wannan kuma ya sabawa dukkan ka’idoji na dimokuradiyya wadanda ta yi wa al’umma alkawarin ingantaciyar rayuwa.

Wannan ba kuma yana nufin cewa, Nijeriya ta taba tsallakawa tudun muntsira ba ne, amma abin da ke tayar da hankali shi ne yadda aka yi wa al’umma alkawari tare da shafa masu romon baka amma kuma sai gashi rayuwa ta zama abin da ta zama, al’umma na fama da yunwa a sassan kasa, ‘yan siyasa sun kasa cika alkawuran da suka yi a lokacin da suke yakin neman zabe.

  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta
  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje

Abubuwan da suka faru a jihohin Neja da Kano da wasu wuraren a sassan Nijeriya alamu ne da su ke nuna cewa, nan gaba kadan ‘yan Nijeriya za su fito su nemai a yi masu adalci saboda daga dukkan alamu ‘yan Nijeriya sun fusata. A yayin da al’umma suka yi kumajin fitowa don nunan rashin amincewarsu da matsalolin da ake fama da su na yunwa da tsadar rayuwa wadanda suke ya kama hanyar durkusar da dukkan sassan tattalin arzikin kasa, to lallai alama ce da ya kamata shugabanni su dauka da muhimmanci.

A Kano, masu zanga-zangar ba suna neman a basu wani abu daban ba ne, suna neman a sama masu abubuwan da zai kawo musu saukin rayuwa ne kamar abinci, saukin kudin makaranta da kuma uwa uba a kawo masu saukin matsalar tsaro da ta addabi al’umma ta yadda za su iya barci ba tare da wata fargaba ba. Sun kuma nemi a bude iyakokin kasa ta yadda za a samu shigo da abinci da sauran kayayyaki don taimaka wajen kawo saikin wadanda ake samar wa a cikin gida.

Idan za a iya tunawa an kulle iyakokin kasar nan ne domin dakile yadda ake shigo da kayan abinci saboda yadda manoma suka yi korafin cewa, shigo da kayan abinci yana durkushe kokarin da suke yi na samar da abinci a cikin gida, amma shin wannan mataki na kulle iyakoki za mu iya cewa, kwalliya ta biya kudin sabulu kuwa?

LABARAI MASU NASABA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

Matsalolin da rufe iyakokin kasar nan ya haifar yana ci gaba da illata al’umma da kuma mummunar shawarar da aka ba gwamnati ta kara kudaden haraji a akan wasu kayan gona da ake shigowa dasu daga kasashen waje. Gwamnati ta sa burin tattaro kudaden haraji koda kuwa mutane za su rasa rayukansu ne. tabbas wadannan manufofin na gwamnati basu da alfanu ga rayuwar al’umma.

A ra’ayinmu, kamar mutum da aka kai shi bango, alamu yana nuna mutane na yi wa manufofin gwamnati tutsu kamar yadda muka gani a wasu sassan Nijeriya a ‘yan kwanakin nan. Ko ‘yan NIjeiya na nuna cewa, takurawar ya isa haka nan ne? wannan kuma yana nuna cewa, duk wanda aka takura ba wanda ya isa ya san abin da zai iya yi na tawaye a nan gaba.

Matsalolin da kulle iyakokin kasar ta haifar da karin haraji a kan kayan abinci da ake shigowa da sun kara tabarbarewar matsalar staro, abin da ya sa manoma basa iya zuwa gonakinsu haka ma in lokacin girbi ya yi sai sun samu izinin ‘yan ta’adda da kuma yadda aka muhimmantar da dala a sha’anin tattalin arzikin kasar nan duk sun jefa al’umma cikin matsaloli da tsadar rayuwa.

Ga dukkan wadanna matsalolin martanin gamnati mai ci bai wadatar ba, sai wai gashi ana cewa, ‘yan Nijeriya cewa, abinci ya fi arhra fiye da koina a Afirka, tabbas wanna karya ne tsagwaronta, muna bukatar sanin wanda ya yi wannan bincike da kuma wace hujjoji ya yi amfani da ita.

Bayan haka kuma sai ga shi kuma ana neman mayar da matsalar ta zama tamkar siyasa, ana neman a ce, ‘yan Nijeriya sun zama wawayen da har sai da ‘yan adawa ne ke amfanai da su wajen bayyana halin da suke ci na matsin rayuwa, wannan abin takaici ne.

Gaskiya a halin yanzu al’umma na cikin yunwa, ‘yan Njjeriya na fuskantar yunwa da suna kuma cikin haushi kuma akwai rudewa na sanin ainihin anihin abin da ya kamata su yi. Amma kuma rikicin shi ne in har aka samu rudewa da yunwa da kuma fushi abubuwa sun lalace, ya kamata gwamnati a dukkan mataki su dauki matakin yayyafawa al’amarin ruwa don kada al’marin ya zama wani abu daban.

Ya kamata kada ‘yan siyasa su raina al’umma, musamman ganin sune suka kai matakin da suke a halin yanzu, ba wai a ce wa talakawa su yi ta hakuri ba tare da jiran tsammani, in har haka gaskiya ne me ya sa su masu tafiyar da mulki wani irin hakuri suke yi a wajen tafiyar da rayuwar su.?

A ra’ayinmu, ya kamata gwamnati ta fuskanci nauyin da al’umma suka dora musu su kuma fahimci cewa tabbas ana fuskantar yunwa a sassan kasa, mutane na mutuwa saboda rashin abinci. Al’umma na kukan yunwa!!

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10
Manyan Labarai

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Next Post
Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa

Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.