ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Na Kukan Yunwa

by Leadership Hausa
2 years ago
Yunwa

A halin yanzu ‘yan Nijeriya, ba tare da banbancin siyasa, addini ko bangaranci ba suna nuna mamakinsu a kan yadda kasar nan ta samu kanta a wannan hali na tabarbarewar tattalin arziki da tsadar rayuwa. Rayuwa ta yi arha amma abin da rayuwar za ta ci ya yi matukar tashi kamar na gwauron zabo, wannan kuma ya sabawa dukkan ka’idoji na dimokuradiyya wadanda ta yi wa al’umma alkawarin ingantaciyar rayuwa.

Wannan ba kuma yana nufin cewa, Nijeriya ta taba tsallakawa tudun muntsira ba ne, amma abin da ke tayar da hankali shi ne yadda aka yi wa al’umma alkawari tare da shafa masu romon baka amma kuma sai gashi rayuwa ta zama abin da ta zama, al’umma na fama da yunwa a sassan kasa, ‘yan siyasa sun kasa cika alkawuran da suka yi a lokacin da suke yakin neman zabe.

  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta
  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje

Abubuwan da suka faru a jihohin Neja da Kano da wasu wuraren a sassan Nijeriya alamu ne da su ke nuna cewa, nan gaba kadan ‘yan Nijeriya za su fito su nemai a yi masu adalci saboda daga dukkan alamu ‘yan Nijeriya sun fusata. A yayin da al’umma suka yi kumajin fitowa don nunan rashin amincewarsu da matsalolin da ake fama da su na yunwa da tsadar rayuwa wadanda suke ya kama hanyar durkusar da dukkan sassan tattalin arzikin kasa, to lallai alama ce da ya kamata shugabanni su dauka da muhimmanci.

ADVERTISEMENT

A Kano, masu zanga-zangar ba suna neman a basu wani abu daban ba ne, suna neman a sama masu abubuwan da zai kawo musu saukin rayuwa ne kamar abinci, saukin kudin makaranta da kuma uwa uba a kawo masu saukin matsalar tsaro da ta addabi al’umma ta yadda za su iya barci ba tare da wata fargaba ba. Sun kuma nemi a bude iyakokin kasa ta yadda za a samu shigo da abinci da sauran kayayyaki don taimaka wajen kawo saikin wadanda ake samar wa a cikin gida.

Idan za a iya tunawa an kulle iyakokin kasar nan ne domin dakile yadda ake shigo da kayan abinci saboda yadda manoma suka yi korafin cewa, shigo da kayan abinci yana durkushe kokarin da suke yi na samar da abinci a cikin gida, amma shin wannan mataki na kulle iyakoki za mu iya cewa, kwalliya ta biya kudin sabulu kuwa?

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Matsalolin da rufe iyakokin kasar nan ya haifar yana ci gaba da illata al’umma da kuma mummunar shawarar da aka ba gwamnati ta kara kudaden haraji a akan wasu kayan gona da ake shigowa dasu daga kasashen waje. Gwamnati ta sa burin tattaro kudaden haraji koda kuwa mutane za su rasa rayukansu ne. tabbas wadannan manufofin na gwamnati basu da alfanu ga rayuwar al’umma.

A ra’ayinmu, kamar mutum da aka kai shi bango, alamu yana nuna mutane na yi wa manufofin gwamnati tutsu kamar yadda muka gani a wasu sassan Nijeriya a ‘yan kwanakin nan. Ko ‘yan NIjeiya na nuna cewa, takurawar ya isa haka nan ne? wannan kuma yana nuna cewa, duk wanda aka takura ba wanda ya isa ya san abin da zai iya yi na tawaye a nan gaba.

Matsalolin da kulle iyakokin kasar ta haifar da karin haraji a kan kayan abinci da ake shigowa da sun kara tabarbarewar matsalar staro, abin da ya sa manoma basa iya zuwa gonakinsu haka ma in lokacin girbi ya yi sai sun samu izinin ‘yan ta’adda da kuma yadda aka muhimmantar da dala a sha’anin tattalin arzikin kasar nan duk sun jefa al’umma cikin matsaloli da tsadar rayuwa.

Ga dukkan wadanna matsalolin martanin gamnati mai ci bai wadatar ba, sai wai gashi ana cewa, ‘yan Nijeriya cewa, abinci ya fi arhra fiye da koina a Afirka, tabbas wanna karya ne tsagwaronta, muna bukatar sanin wanda ya yi wannan bincike da kuma wace hujjoji ya yi amfani da ita.

Bayan haka kuma sai ga shi kuma ana neman mayar da matsalar ta zama tamkar siyasa, ana neman a ce, ‘yan Nijeriya sun zama wawayen da har sai da ‘yan adawa ne ke amfanai da su wajen bayyana halin da suke ci na matsin rayuwa, wannan abin takaici ne.

Gaskiya a halin yanzu al’umma na cikin yunwa, ‘yan Njjeriya na fuskantar yunwa da suna kuma cikin haushi kuma akwai rudewa na sanin ainihin anihin abin da ya kamata su yi. Amma kuma rikicin shi ne in har aka samu rudewa da yunwa da kuma fushi abubuwa sun lalace, ya kamata gwamnati a dukkan mataki su dauki matakin yayyafawa al’amarin ruwa don kada al’marin ya zama wani abu daban.

Ya kamata kada ‘yan siyasa su raina al’umma, musamman ganin sune suka kai matakin da suke a halin yanzu, ba wai a ce wa talakawa su yi ta hakuri ba tare da jiran tsammani, in har haka gaskiya ne me ya sa su masu tafiyar da mulki wani irin hakuri suke yi a wajen tafiyar da rayuwar su.?

A ra’ayinmu, ya kamata gwamnati ta fuskanci nauyin da al’umma suka dora musu su kuma fahimci cewa tabbas ana fuskantar yunwa a sassan kasa, mutane na mutuwa saboda rashin abinci. Al’umma na kukan yunwa!!

Yunwa
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa

Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.