• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan ta’adda Sun Kashe Monoman Shinkafa 15, Da Tarwatsa Wasu Da Dama A Jihar Borno

by Muhammad
2 years ago
Borno

Wasu gungun ‘yan ta’addan da ake zaton ‘yan kungiyar Boko Haram ne, a ranar Lahadi, sun kai wani mummunar hari kan manoman shinkafa da ke yankin Zabarmari a lokacin da suke aikin noman shinkafa a karamar hukumar Mafa ta jihar Borno, inda suka kashe sama da mutum 15.

Wani manomin shinkafa, Awali Casa, ya tabbatar wa jaridar LEADERSHIP cewa, harin da aka kai ya sanya fargaba a zukatan manoman yankin na Zabarmari.

  • Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno
  • Sojoji Sun Yi Ruwan Wuta Kan ‘Yan Ta’adda, Sun Halaka 160 A Borno Da Yobe

Awali ya ce, yanzu haka ana ci gaba da neman gawarwakin manoman da ‘yan ta’addar suka halaka a gonakinsu na shinkafa, an kuma laluben sauran mutanen da suka bace yayin kai harin.

LEADERSHIP ta rawaito cewa ‘yan ta’addar dauke da muggan makamai sun kai harin ne kan gonakin inda suka nufi manoman shinkafa da suke aikin girbi a kauyukan Koshebe da Karkut da Bulabulin da ke karamar hukumar Mafa ta jihar Borno, yankin ke da tazarar kilomita 20 daga Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

Wani masani kan yaki da ‘yan tayar da kayar baya kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi, Zagazola Makama, ya ce ‘yan ta’addar sun kai harin ne kan babura inda suka raba kawunansu gida uku kafin su kai hari kan manoman.

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Wannan majiyar ta ce ‘yan ta’addar ba su yi amfani da bindigu ba, sai dai sun yi amfani da wukake inda suka yi wa manoman yankan rago da sassara su.

“An gano akalla gawarwaki tara har zuwa daren ranar Lahadi, yayin da ake ci gaba da neman wasu da suka yi gudun tsira da ransu daga harin ‘yan ta’addar,” cewar Makama.

Idan dai za a iya tunawa ‘yan ta’addar Boko Haram a shekaru uku da suka gabata sun kashe manoman shinkafa sama da 76 a kauyen Zabarmari da ke karamar hukumar Jere a jihar.

Harin da aka da ‘yan ta’addar suka kai na bayannan sun ce sun kashe manoman shinkafa da dama, kuma yana a matsayin jan kunne ga manoman da kuma rundunar sojojin Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026
Manyan Labarai

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba
Ilimi

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
Manyan Labarai

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

October 13, 2025
Next Post
Kotun Daukaka Karar Zaben Gwamnan Kano Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci Kan Shari’ar

Kotun Daukaka Karar Zaben Gwamnan Kano Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci Kan Shari'ar

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

October 13, 2025
Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

October 13, 2025
Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.