• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan ta’adda Sun Kashe Monoman Shinkafa 15, Da Tarwatsa Wasu Da Dama A Jihar Borno

by Muhammad
2 years ago
Borno

Wasu gungun ‘yan ta’addan da ake zaton ‘yan kungiyar Boko Haram ne, a ranar Lahadi, sun kai wani mummunar hari kan manoman shinkafa da ke yankin Zabarmari a lokacin da suke aikin noman shinkafa a karamar hukumar Mafa ta jihar Borno, inda suka kashe sama da mutum 15.

Wani manomin shinkafa, Awali Casa, ya tabbatar wa jaridar LEADERSHIP cewa, harin da aka kai ya sanya fargaba a zukatan manoman yankin na Zabarmari.

  • Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno
  • Sojoji Sun Yi Ruwan Wuta Kan ‘Yan Ta’adda, Sun Halaka 160 A Borno Da Yobe

Awali ya ce, yanzu haka ana ci gaba da neman gawarwakin manoman da ‘yan ta’addar suka halaka a gonakinsu na shinkafa, an kuma laluben sauran mutanen da suka bace yayin kai harin.

LEADERSHIP ta rawaito cewa ‘yan ta’addar dauke da muggan makamai sun kai harin ne kan gonakin inda suka nufi manoman shinkafa da suke aikin girbi a kauyukan Koshebe da Karkut da Bulabulin da ke karamar hukumar Mafa ta jihar Borno, yankin ke da tazarar kilomita 20 daga Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

Wani masani kan yaki da ‘yan tayar da kayar baya kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi, Zagazola Makama, ya ce ‘yan ta’addar sun kai harin ne kan babura inda suka raba kawunansu gida uku kafin su kai hari kan manoman.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

Wannan majiyar ta ce ‘yan ta’addar ba su yi amfani da bindigu ba, sai dai sun yi amfani da wukake inda suka yi wa manoman yankan rago da sassara su.

“An gano akalla gawarwaki tara har zuwa daren ranar Lahadi, yayin da ake ci gaba da neman wasu da suka yi gudun tsira da ransu daga harin ‘yan ta’addar,” cewar Makama.

Idan dai za a iya tunawa ‘yan ta’addar Boko Haram a shekaru uku da suka gabata sun kashe manoman shinkafa sama da 76 a kauyen Zabarmari da ke karamar hukumar Jere a jihar.

Harin da aka da ‘yan ta’addar suka kai na bayannan sun ce sun kashe manoman shinkafa da dama, kuma yana a matsayin jan kunne ga manoman da kuma rundunar sojojin Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Next Post
Kotun Daukaka Karar Zaben Gwamnan Kano Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci Kan Shari’ar

Kotun Daukaka Karar Zaben Gwamnan Kano Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci Kan Shari'ar

LABARAI MASU NASABA

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.