• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Daukaka Karar Zaben Gwamnan Kano Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci Kan Shari’ar

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
Kotun Daukaka Karar Zaben Gwamnan Kano Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci Kan Shari’ar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta yi zamanta na farko kan sauraren karar da gwamnan jihar Kano, Abba K. Yusuf ya shigar kan hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe ta jihar ta yanke na tsige shi daga kujerar gwamna da tabbatar da Dr. Nasiru Gawuna a matsayin wanda ya yi nasara.

Idan dai baku manta ba, kotun sauraren korafe-korafen zaben Gwamnan Kano mai alkalai uku a karkashin mai shari’a Oluyemi Akintan Osadebay ta tsige Abba K. Yusuf daga kujerar gwamnan Kano a ranar 20 ga watan Satumba, 2023, bayan kotun ta zare kuri’u 165,663 da ta ce ba su cika ka’idar zama halastattun kuri’u ba.

  • DA DUMI-DUMI: Kotu Ta Kori Gwamna Abba Gida-Gida Ta Tabbatar Da Nasarar Gawuna
  • NNPP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Sauraren Karar Zaben Gwamnan Kano Da Ta Ba Gawuna Nasara

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta sanar da Abba Yusuf wanda a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga Maris, 2023, inda ta ce ya samu kuri’u 1,019,602 inda ya doke Gawuna na APC da kuri’u 890,705.

Sai dai jam’iyyar APC ta tunkari Kotun, bisa zargin tafka kura-kurai da magudin zabe.

Kotun ta karbi korafin da APC ta shigar inda ta soke zaben Yusuf, da dalilan cewa sama da kuri’u zabe 160,000 INEC ba ta sanya hannu da tambari da kwanan wata ba.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

An rage kuri’un Yusuf zuwa 853,939 yayin da kuri’u 890,705 Ganuwa suke a yadda suke tun asali.

Daga bisani gwamnan ya shigar da kara a gaban kotun daukaka kara.

Jam’iyyun APC da INEC, da NNPP su ma sun shigar da kara a gaban kotun.

A ranar Litinin, babban lauyan gwamnan, Wole Olanipekun SAN (wanda shi ne babban lauyan Tinubu a PEPC), ya bukaci kotun daukaka karar da ta ajiye hukuncin da kotun sauraren korafe-korafen zabe ta yanke a baya.

Olanipekun ya bayar da hujjar cewa kotun sauraren korafe-korafen zaben gwamnan ta kirkiro wasu sabbin sharudda wadanda suka fita daga dukkan hukunce-hukuncen da kotun daukaka kara ko kotun koli ta yanke.

Dangane da batun kuri’un zabe kuwa, ya ce wannan shi ne karo na farko a tarihin kotun da wata kotu za ta soke zabe kan rashin sanya hannu a bayan kuri’un zabe.

Olanipekun ya bayar da hujjar cewa bai kamata a bar hukuncin da kotun sauraren korafe-korafen zaben gwamnan ta yanke ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaGawunaKotun Daukaka Kara
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan ta’adda Sun Kashe Monoman Shinkafa 15, Da Tarwatsa Wasu Da Dama A Jihar Borno

Next Post

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Farko Na Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Kan Musayar Kimiyya Da Fasaha

Related

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

2 hours ago
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

3 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

13 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

16 hours ago
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

22 hours ago
Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon
Manyan Labarai

Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon

24 hours ago
Next Post
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Farko Na Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Kan Musayar Kimiyya Da Fasaha

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Farko Na Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Kan Musayar Kimiyya Da Fasaha

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.