ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan ta’adda Sun Kashe Monoman Shinkafa 15, Da Tarwatsa Wasu Da Dama A Jihar Borno

by Muhammad
3 years ago
Borno

Wasu gungun ‘yan ta’addan da ake zaton ‘yan kungiyar Boko Haram ne, a ranar Lahadi, sun kai wani mummunar hari kan manoman shinkafa da ke yankin Zabarmari a lokacin da suke aikin noman shinkafa a karamar hukumar Mafa ta jihar Borno, inda suka kashe sama da mutum 15.

Wani manomin shinkafa, Awali Casa, ya tabbatar wa jaridar LEADERSHIP cewa, harin da aka kai ya sanya fargaba a zukatan manoman yankin na Zabarmari.

  • Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno
  • Sojoji Sun Yi Ruwan Wuta Kan ‘Yan Ta’adda, Sun Halaka 160 A Borno Da Yobe

Awali ya ce, yanzu haka ana ci gaba da neman gawarwakin manoman da ‘yan ta’addar suka halaka a gonakinsu na shinkafa, an kuma laluben sauran mutanen da suka bace yayin kai harin.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP ta rawaito cewa ‘yan ta’addar dauke da muggan makamai sun kai harin ne kan gonakin inda suka nufi manoman shinkafa da suke aikin girbi a kauyukan Koshebe da Karkut da Bulabulin da ke karamar hukumar Mafa ta jihar Borno, yankin ke da tazarar kilomita 20 daga Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

Wani masani kan yaki da ‘yan tayar da kayar baya kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi, Zagazola Makama, ya ce ‘yan ta’addar sun kai harin ne kan babura inda suka raba kawunansu gida uku kafin su kai hari kan manoman.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Wannan majiyar ta ce ‘yan ta’addar ba su yi amfani da bindigu ba, sai dai sun yi amfani da wukake inda suka yi wa manoman yankan rago da sassara su.

“An gano akalla gawarwaki tara har zuwa daren ranar Lahadi, yayin da ake ci gaba da neman wasu da suka yi gudun tsira da ransu daga harin ‘yan ta’addar,” cewar Makama.

Idan dai za a iya tunawa ‘yan ta’addar Boko Haram a shekaru uku da suka gabata sun kashe manoman shinkafa sama da 76 a kauyen Zabarmari da ke karamar hukumar Jere a jihar.

Harin da aka da ‘yan ta’addar suka kai na bayannan sun ce sun kashe manoman shinkafa da dama, kuma yana a matsayin jan kunne ga manoman da kuma rundunar sojojin Nijeriya.

Borno
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Next Post
Kotun Daukaka Karar Zaben Gwamnan Kano Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci Kan Shari’ar

Kotun Daukaka Karar Zaben Gwamnan Kano Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci Kan Shari'ar

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.