• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Tawayen RSF Sun Kashe Mutane 25 A Sudan

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
in Tsaro
0
‘Yan Tawayen RSF Sun Kashe Mutane 25 A Sudan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutum 25 ne suka mutu, sannan gommai suka jikkata a harin da dakarun ‘yan tawaye na RSF suka kai a sansann ‘yan gudun hijira da ke Abu Shouk da Birnin al-Fashir da ke Yammacin Sudan.

“Jami’in Ma’aikatar Lafiya Ibrahim Khater ya ce mutum 25 sun mutu, sannan mutum 40 suka jikkata a harin na sansanin ‘yan gudun hijira na Abu Shouk, inda akwai kusan mutum 400,000 da suke zaman gudun hijira a sansanin,” kamar yadda jaridar Tribun mai zaman kanta a Sudan ta ruwaito a tsakiyar makon nan.

  • Motocin Agaji Sun Shiga Sudan Daga Chadi A Karon Farko
  • Sin Ta Yi Kira Ga Gamayyar Kasa Da Kasa Da Su Mutunta ’Yancin Kan Sudan Ta Kudu A Lokacin Mulkin Rikon Kwarya

Jaridar ta kara da cewa, “ganau sun kuma ce dakarun na RSF sun yi luguden wuta a gidajen mutane da asibitin ‘yansanda, wanda ya tilasta aka rufe asibitin.”

RSF ba ta ce komai a kan kisan ba.

An dade ana zargin kungiyar da kisan kan mai uwa da wabi a al-Fashir, inda yakin ya kashe daruruwan mutane tun bayan farkonsa a 10 ga Mayu, sannan mutane da dama suke tsere.

Labarai Masu Nasaba

Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Watanni ke nan Al-Fashir na karkashin dakarun RSF, inda yanzu haka ake fargabar shiga karancin abinci da magunguna.

A wani labarin kuma, Ma’aikatar lafiya a Sudan ta tabbatar da mutuwar mutane 132, sakamakon ambaliyar ruwan da mamakon ruwan saman da ba a taba gani ba cikin shekara guda ya haddasa a kasar.

Hukumomi sun ce ambaliyar ruwan ta shafi jihohi 10, ya yin da kusan mutum dubu 130 da yakin basasar da ake yi a kasar ya raba da muhallansu.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce a gabashin Jihar Bahrul Ahmar, mutum 33 ne suka mutu bayan wata madatsar ruwa ta balle saboda tumbatsar da ruwan ya yi.

Ta yi gargadin adadin ka iya fin haka sakamakon har yanzu akwai wadanda suka bata ba a gano su ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NigeriaSudanWar
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Sa Hotona A Soshiyal Midiya Suna Yabo Babu Abin Da Za Su Samu – Hadiza Gabon

Next Post

Nijar Za Ta Fara Tattara Bayanan ‘Yan Ta’adda

Related

Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo
Tsaro

Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

2 hours ago
Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato
Tsaro

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

5 days ago
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga 3, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace
Tsaro

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga 3, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace

2 weeks ago
Ana Zargin Wani Ɗansanda Da Kisan Wata Mata Kan Cin Hancin Naira 2,000 — Bincike
Tsaro

‘Yansandan Sun Kama Wanda ake Zargi Da Satar Mutane A Sokoto

2 weeks ago
Dole Jama’a Su Marawa Sojoji  Baya Don Samun Nasara A Yaƙi Da Ƴan Ta’adda
Tsaro

Dole Jama’a Su Marawa Sojoji  Baya Don Samun Nasara A Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

2 weeks ago
Ƴan Fashi Sun Sace Fasinjoji 7, Ƴansanda Sun Ceto 2 A Kwara
Tsaro

Ƴan Fashi Sun Sace Fasinjoji 7, Ƴansanda Sun Ceto 2 A Kwara

3 weeks ago
Next Post
Nijar Za Ta Fara Tattara Bayanan ‘Yan Ta’adda

Nijar Za Ta Fara Tattara Bayanan ‘Yan Ta’adda

LABARAI MASU NASABA

Zargin Cin Zarafi: Gaskiyar Halin Da Ake Ciki A Gidan Yarin Goron Dutse

Zargin Cin Zarafi: Gaskiyar Halin Da Ake Ciki A Gidan Yarin Goron Dutse

May 16, 2025
Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista

Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista

May 16, 2025
Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

May 16, 2025
Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

May 16, 2025
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

May 16, 2025
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

May 16, 2025
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

May 16, 2025
Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.