• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yandaba Sun Kawo Cikas Ana Tsaka Da Gudanar Da Yakin Neman Zaben APC A Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
'Yandaba

Daruruwan ‘Yandabar siyasa sun kawo cikas a yakin neman zaben jam’iyyar APC na shiyya ta uku da yammacin ranar Asabar, a garin Gashuwa, shalkwatar karamar hukumar Bade da ke jihar Yobe, mahaifar shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya.

An tsara aiwatar da taron gangamin yakin neman zaben ne bayan bude sabuwar kasuwar zamani wadda gwamnan jihar, Hon. Mai Mala Buni ya gina a garin Nguru, inda daga bisani aka hallara a Filin Agric da ke unguwar Katuzu a Gashuwa.

  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Ahmad Lawan A Matsayin Dan Takarar APC A Yobe Ta Arewa
  • Wa’adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci

Bugu da kari kuma, tun a garin Nguru aka fara ganin alamun yiwa tawagar ‘yan siyasar ture, kana kuma kafin shiga garin da zuwa inda aka shirya gudanar da taron, wasu gungun fusatattun matasa ne suka tsaya kan hanya suna yi wa tawagar ‘yan siyasar ihu da rashin arziki akan hanya.

Abun ya kara kamari ne a lokacin da shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmed Ibrahim Lawan, yake kokarin mika abin magana ga gwamna Mai Mala Buni, wanda yake tare da gwamna Inuwa Yahaya na jihar Gombe, inda kan ka ce kwabo, fusatattun matasan suka rinka shewa da ihun: ‘ba ma yi, ba ma yi, ba ma so’ tare da jifa kan mai uwa da wabi kan dandamalin da manyan baki suke tsaye a kai.

Haka zalika, an sha dage ranar da za a gudanar wannan yakin zaben a jihar, sakamakon rashin tabbas da rudanin da APC ta shiga a jihar. Al’amarin da ya samo asali daga rikita-rikitar da ta dabaibaye zaben fidda-gwanin da jam’iyyar APC ta gudanar a jihar, da kuma hukuncin da kotun koli ta yanke kan takarar kujerar Sanatan Yobe ta Arewa; duk suna daga cikin abubuwan da suka tunzura wasu matasa.

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

Kazalika, wannan gangamin taron yakin neman zaben ya samu halartar dubun-dubatar magoya bayan jam’iyyar APC a fadin jihar, wanda ya kunshi jiga-jigan mutane, wadanda suka hada da shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan, gwamna Mai Mala Buni tare da Mataimakinsa, gwamnan jihar Gombe, Alhaji Inuwa Yahaya da shugabanin jam’iyyar APC a jihar Yobe da kwamitin yakin neman zaben 2023 da sauran su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
'Yandaba
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta
Siyasa

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
Next Post
Nijeriya

Bambancin Halin Da ‘Yan Nijeriya Suka Shiga A Canjin Kudin Buhari Na Farko Da Na Biyu

LABARAI MASU NASABA

Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025
Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.