• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yandaba Sun Kawo Cikas Ana Tsaka Da Gudanar Da Yakin Neman Zaben APC A Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Siyasa
0
‘Yandaba Sun Kawo Cikas Ana Tsaka Da Gudanar Da Yakin Neman Zaben APC A Yobe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daruruwan ‘Yandabar siyasa sun kawo cikas a yakin neman zaben jam’iyyar APC na shiyya ta uku da yammacin ranar Asabar, a garin Gashuwa, shalkwatar karamar hukumar Bade da ke jihar Yobe, mahaifar shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya.

An tsara aiwatar da taron gangamin yakin neman zaben ne bayan bude sabuwar kasuwar zamani wadda gwamnan jihar, Hon. Mai Mala Buni ya gina a garin Nguru, inda daga bisani aka hallara a Filin Agric da ke unguwar Katuzu a Gashuwa.

  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Ahmad Lawan A Matsayin Dan Takarar APC A Yobe Ta Arewa
  • Wa’adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci

Bugu da kari kuma, tun a garin Nguru aka fara ganin alamun yiwa tawagar ‘yan siyasar ture, kana kuma kafin shiga garin da zuwa inda aka shirya gudanar da taron, wasu gungun fusatattun matasa ne suka tsaya kan hanya suna yi wa tawagar ‘yan siyasar ihu da rashin arziki akan hanya.

Abun ya kara kamari ne a lokacin da shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmed Ibrahim Lawan, yake kokarin mika abin magana ga gwamna Mai Mala Buni, wanda yake tare da gwamna Inuwa Yahaya na jihar Gombe, inda kan ka ce kwabo, fusatattun matasan suka rinka shewa da ihun: ‘ba ma yi, ba ma yi, ba ma so’ tare da jifa kan mai uwa da wabi kan dandamalin da manyan baki suke tsaye a kai.

Haka zalika, an sha dage ranar da za a gudanar wannan yakin zaben a jihar, sakamakon rashin tabbas da rudanin da APC ta shiga a jihar. Al’amarin da ya samo asali daga rikita-rikitar da ta dabaibaye zaben fidda-gwanin da jam’iyyar APC ta gudanar a jihar, da kuma hukuncin da kotun koli ta yanke kan takarar kujerar Sanatan Yobe ta Arewa; duk suna daga cikin abubuwan da suka tunzura wasu matasa.

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Kazalika, wannan gangamin taron yakin neman zaben ya samu halartar dubun-dubatar magoya bayan jam’iyyar APC a fadin jihar, wanda ya kunshi jiga-jigan mutane, wadanda suka hada da shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan, gwamna Mai Mala Buni tare da Mataimakinsa, gwamnan jihar Gombe, Alhaji Inuwa Yahaya da shugabanin jam’iyyar APC a jihar Yobe da kwamitin yakin neman zaben 2023 da sauran su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YandabaAhmad lawanMai MalaSiyasaYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shawara Da Gargadi Ga Matan Facebook A Kan Tsiraici (Uwargida)

Next Post

Bambancin Halin Da ‘Yan Nijeriya Suka Shiga A Canjin Kudin Buhari Na Farko Da Na Biyu

Related

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

8 hours ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

3 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

4 days ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

7 days ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

1 week ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

1 week ago
Next Post
Nijeriya

Bambancin Halin Da ‘Yan Nijeriya Suka Shiga A Canjin Kudin Buhari Na Farko Da Na Biyu

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.