• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yandaba Sun Kawo Cikas Ana Tsaka Da Gudanar Da Yakin Neman Zaben APC A Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
'Yandaba

Daruruwan ‘Yandabar siyasa sun kawo cikas a yakin neman zaben jam’iyyar APC na shiyya ta uku da yammacin ranar Asabar, a garin Gashuwa, shalkwatar karamar hukumar Bade da ke jihar Yobe, mahaifar shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya.

An tsara aiwatar da taron gangamin yakin neman zaben ne bayan bude sabuwar kasuwar zamani wadda gwamnan jihar, Hon. Mai Mala Buni ya gina a garin Nguru, inda daga bisani aka hallara a Filin Agric da ke unguwar Katuzu a Gashuwa.

  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Ahmad Lawan A Matsayin Dan Takarar APC A Yobe Ta Arewa
  • Wa’adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci

Bugu da kari kuma, tun a garin Nguru aka fara ganin alamun yiwa tawagar ‘yan siyasar ture, kana kuma kafin shiga garin da zuwa inda aka shirya gudanar da taron, wasu gungun fusatattun matasa ne suka tsaya kan hanya suna yi wa tawagar ‘yan siyasar ihu da rashin arziki akan hanya.

Abun ya kara kamari ne a lokacin da shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmed Ibrahim Lawan, yake kokarin mika abin magana ga gwamna Mai Mala Buni, wanda yake tare da gwamna Inuwa Yahaya na jihar Gombe, inda kan ka ce kwabo, fusatattun matasan suka rinka shewa da ihun: ‘ba ma yi, ba ma yi, ba ma so’ tare da jifa kan mai uwa da wabi kan dandamalin da manyan baki suke tsaye a kai.

Haka zalika, an sha dage ranar da za a gudanar wannan yakin zaben a jihar, sakamakon rashin tabbas da rudanin da APC ta shiga a jihar. Al’amarin da ya samo asali daga rikita-rikitar da ta dabaibaye zaben fidda-gwanin da jam’iyyar APC ta gudanar a jihar, da kuma hukuncin da kotun koli ta yanke kan takarar kujerar Sanatan Yobe ta Arewa; duk suna daga cikin abubuwan da suka tunzura wasu matasa.

LABARAI MASU NASABA

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Kazalika, wannan gangamin taron yakin neman zaben ya samu halartar dubun-dubatar magoya bayan jam’iyyar APC a fadin jihar, wanda ya kunshi jiga-jigan mutane, wadanda suka hada da shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan, gwamna Mai Mala Buni tare da Mataimakinsa, gwamnan jihar Gombe, Alhaji Inuwa Yahaya da shugabanin jam’iyyar APC a jihar Yobe da kwamitin yakin neman zaben 2023 da sauran su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
Siyasa

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

October 11, 2025
Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

October 11, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Next Post
Nijeriya

Bambancin Halin Da ‘Yan Nijeriya Suka Shiga A Canjin Kudin Buhari Na Farko Da Na Biyu

LABARAI MASU NASABA

Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana

Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana

October 13, 2025
Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

October 13, 2025
Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

October 13, 2025
Asuu

Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 

October 13, 2025
hisba

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

October 13, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Nijeriya

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

October 13, 2025
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

October 13, 2025
nema

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

October 13, 2025
Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.