ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa’adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci

Ya Ce A Cikin Kananan Hukumomin Jihar 17, 4 Kacal Suke Da Banki

by Muhammad Maitela
3 years ago
cbn

Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni, ya bukaci Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya kara wa al’ummar jihar Yobe wa’adi na daban, da zai bayar da damar canza tsoffin takardun kudadensu, sabanin 31 ga watan Janairun da ya saka da farko.

Gwamnan ya bayyana hakan a sanarwar manema labaru, ranar Lahadi, mai dauke da sa-hannun Daraka Janar kan hulda da yan jaridu da Kafafen yada labaru, Mamman Mohammed, inda ya ce Gwamna Buni ya bayyana cewa neman ƙarin wa’adin ya zama dole sakamakon yadda jihar ke fama da karancin bankuna.

Gwamna Buni ya kara da cewa, kananan hukumomi hudu ne kacal cikin 17, a fadin jihar suke da bankuna, al’amarin da ya ce zai yi wahala mutane su samu damar canja kudaden su a kwanaki 13 da suka rage a wa’adin da Babban Bankin Nijeriya ya gindaya.

ADVERTISEMENT

“Sannan kuma wasu daga cikin bankunan da suke da rassa a wasu kananan hukumomin, dole ya sa sun rufe sakamakon rikicin Boko Haram da ya yi kamari, kuma har yanzu basu sake bude su ba a fadin jihar.”

“Saboda haka muna kyautata zaton CBN zai kula wajen bai wa irin wadannan wurare kulawa ta musamman sakamakon bukatu na musamman, domin kaucewa jawo asarar kudaden jama’a.”

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

“Kuma muna kira ga CBN da sauran bankunan Kasuwanci su kalli wannan bukata ta jama’a cikin gaggawa wajen nemawa al’umma mafita tare da dakile halin fargaban da ake ciki.”

“A matsayinsa na mai sanya ido, yana da kyau Babban Bankin Nijeriya ya tabbatar cewa bankunan Kasuwanci sun bude rassan su a shalkwatar kananan hukumomin saboda a halin yanzu zaman lafiya ya samu a fadin jihar Yobe.” In ji Gwamna.

  • Naja’atu Ta Yi Murabus Daga Kwamitin Yakin Zaben Tinubu, Ta Fice Daga APC

 

Bugu da kari, Gwamna Buni ya kara da cewa, ci gaban da ake samu ta fannin tsaro a jihar Yobe da Arewa Maso Gabas baki daya, babu wata fargabar da za ta hana bankuna su sake bude rassan su a shalkwatar kananan hukumomin da manyan garuruwa.

Har ila yau, Gwamna Buni ya sake nanata cewa, akwai fargaba matikar ba a dauki matakin gaggawa ba, saboda ko shakka babu jama’a da dama za su fuskanci barazanar karayar tattalin arziki, da dalilin canjin kudin.

  • https://leadership.ng/cbn-warns-against-rejection-of-old-naira-notes/

 

“Sannan a matsayinmu na gwamnati, wajibi ne mu yi dogon nazari don kaucewa kalubalen da zai jawo, wanda lalle akwai bukatar CBN, Babban Bankin Nijeriya ya dubi lamarin nan tare da daukar matakan da suka dace wajen shawo kan matsalar.” In ji Gwamna Buni.

cbn
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
An Yi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Zomo Ta Kasar Sin A Fadin Duniya

An Yi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Zomo Ta Kasar Sin A Fadin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.