Zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, Fu Cong, ya bayyana a gun taron gaggawa game da batun Kongo(Kinshasa) da kwamitin sulhu ya kira jiya Talata cewa, a halin yanzu, yankin gabashin Kongo(Kinshasa) yana cikin yanayi mai hadari. Ya ce Sin na goyon bayan mambobin kwamitin sulhu su hada kai tare da daukar kwararan matakai, ta yadda za a samar da dabarun hana yanayin ya ci gaba da tsanani da kuma inganta warware batun a siyasance.
Fu Cong ya bayyana cewa, kwanan nan, yanayin Kongo(Kinshasa) ya shiga matsanancin yanayi ciki sauri, inda kungiyar M23 ta kai hari birnin Goma, hedkwatar jihar Kivu ta arewa dake kasar, lamarin da ya sanya fararen hula da yawa barin gidajensu, inda kuma hadarin barkewar rikici mai girma ke karuwa, wanda ke zaman abun damuwa matuka.
- Gwamna Nasir Ya Ƙaddamar da Aikin Titin Koko–Zuru Kan Naira Biliyan 64
- Fashewar Tayar Jirgi A Kano: Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kamfanin Max Air Na Tsawon Watanni Uku
Ya nanata cewa, Sin za ta dage wajen goyon bayan ikon mulkin Kongo(Kinshasa) da mallakar cikakkun yankunanta, kuma tana adawa da dukkanin abubuwan dake keta tsarin dokokin MDD da dokokin kasa da kasa. Haka zalika, bangaren Sin yana bukatar kungiyar M23 ta daina dukkanin ayyukan nuna adawa, kuma ta janye daga yankunan da ta mamaye, kamar Goma.
Fu Cong ya kara da cewa, bangaren Sin yana tir da harin M23 kan ma’aikatan wanzar da zaman lafiya na MDD, kuma yana goyon bayan tawagar MDD dake Kongo(Kinshasa) ta gudanar da ayyukan kare fararen hula, karkashin amincewar kwamitin sulhun. Ya kuma jadadda cewa, babu wata hanyar bude wuta da za ta magance batun gabashin Kongo (Kinshasa), tattaunawa ta diflomasiyya ce kawai mafita. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp