ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Nasir Ya Ƙaddamar da Aikin Titin Koko–Zuru Kan Naira Biliyan 64

by Umar Faruk
1 year ago
Titin

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya ƙaddamar da aikin shimfiɗa titin Koko zuwa Dabai da ke Ƙaramar Hukumar Zuru, wanda zai ci Naira biliyan 64.

Aikin zai gudana ne ƙarƙashin kamfanoni uku, kuma ana sa ran za a kammala shi cikin watanni 18.

  • Sojoji Sun Ƙwato Makamai, Sun Ci Gaba Da Neman Bello Turji A Zamfara
  • Wa’adin Ficewar Nijar, Mali Da Burkina Faso Daga ECOWAS Ya Cika Yau

Hanyar, wacce ta kai tsawon kilomita 87, ta kasance mallakar gwamnatin tarayya.

ADVERTISEMENT

Sai dai saboda jinkirin aiki, an soke kwangilar baya, kuma hukumomin tarayya sun bayar da dama ga gwamnatin Kebbi ta ɗauki nauyin aikin, tare da alƙawarin mayar mata da kuɗaɗen da ta kashe bayan an kammala aikin.

Gwamna Nasir ya bayyana cewa, ko da gwamnatin tarayya ta biya ko ba ta biya ba, gwamnatinsa za ta ɗauki nauyin aikin, ganin yadda titin ke da matuƙar muhimmanci ga al’ummar jihar da ma Nijeriya baki ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Aike Da Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi Zuwa Majalisar Dattawa

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2 Tare Da Kama Wasu A Kaduna

Ya gargaɗi kamfanonin da suka samu kwangilar da su tabbatar da ingantaccen aiki, tare da jaddada cewa za a hukunta duk wanda ya kasa cika sharuɗan aikin.

Sannan, ya buƙaci direbobin manyan motoci da su guji lodin da ya fi ƙarfin titin domin kare lafiyar matafiya da rage hatsari.

Don haka, gwamnati za ta kafa kwamiti don tabbatar da bin doka da oda a kan titin.

Kwamishinan ayyuka na jihar, Injiniya Abdullahi Umar Faruk, ya bayyana cewa kashi 40 na kuɗin aikin an riga an biya.

Ya ce an biya kamfanonin kuɗin kamar haka:

  • Kamfanin ZBBC zai shimfiɗa titin daga Dabai zuwa Mahuta (kilomita 25) a kan Naira biliyan 18.
  • Kamfanin Habib Engineering LTD zai yi aikin daga Mahuta zuwa Marafa (kilomita 25) a kan Naira biliyan 18.
  • Kamfanin GNIC zai yi aikin daga Koko zuwa Marafa (kilomita 37) a kan Naira biliyan 27.

Baya ga titin Koko – Zuru, Gwamna Idris ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar za ta inganta babban asibitin Zuru domin ya zama cibiyar ƙwararru.

Haka nan, a yayin ziyarar godiya da ya kai ƙananan hukumomin Fakai, Sakaba, Danko Wasagu, da Zuru, ya kuma ƙaddamar da wata hanyar karkara mai tsawon kilomita 11 daga Koko zuwa garin Kangin Korama, wanda aikin zai ci Naira biliyan 1.3.

Titin
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata
Manyan Labarai

Tinubu Ya Aike Da Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi Zuwa Majalisar Dattawa

June 23, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato
Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2 Tare Da Kama Wasu A Kaduna

June 23, 2026
‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja
Manyan Labarai

Yadda Lakurawa Suka tare Babbar Hanyar Zuwa Neja, Tare Da Jefa Jama’a Cikin Firgici

June 23, 2026
Next Post
Alkaluman Watsa Shirye-Shiryen Shagalin Bikin Bazara Na CMG Na 2025 Sun Kai Sabon Matsayi

Alkaluman Watsa Shirye-Shiryen Shagalin Bikin Bazara Na CMG Na 2025 Sun Kai Sabon Matsayi

LABARAI MASU NASABA

Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata

Tinubu Ya Aike Da Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi Zuwa Majalisar Dattawa

June 23, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2 Tare Da Kama Wasu A Kaduna

June 23, 2026
‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Yadda Lakurawa Suka tare Babbar Hanyar Zuwa Neja, Tare Da Jefa Jama’a Cikin Firgici

June 23, 2026
Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Watsi Da Kiran Obi Na Buƙatar Tinubu Ya Yi Murabus

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Watsi Da Kiran Obi Na Buƙatar Tinubu Ya Yi Murabus

June 23, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 47 Da ISWAP Suka Sace A Jihar Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 47 Da ISWAP Suka Sace A Jihar Borno

June 23, 2026
’Yan Bindiga Sun Sace Matafiya 28 A Jihar Filato

An Kashe Mutane 19 A Wani Sabon Hari A Filato

June 23, 2026
Jami’an Tsaro Sun Kama Mutane 3 Da Makamai A Kogi

Jami’an Tsaro Sun Kama Mutane 3 Da Makamai A Kogi

June 23, 2026
Tinubu Ya Yi Murabus Saboda Ya Gaza A Kan Matsalar Tsaro – Peter Obi

Tinubu Ya Yi Murabus Saboda Ya Gaza A Kan Matsalar Tsaro – Peter Obi

June 23, 2026
An Bude Bikin Baje Kolin Hada-Hadar Samar Da Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Karo Na Hudu

An Bude Bikin Baje Kolin Hada-Hadar Samar Da Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Karo Na Hudu

June 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.