• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
Yansanda

Rundunar ‘Yansandan Jihar Gombe ta bayyana cewa ta kwato tarin miyagun kwayoyi bayan wata nasarar samame da ta kai a maboyar ‘yan ta’adda da ake zargi, da ke bayan wani katafaren kanti na ‘Gombe Local Government Shopping Complex’.

 

Wannan bayani ya fito a cikin wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na ‘yansanda, DSP Buhari Abdullahi, ya sanya hannu a kai.

  • Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul
  • JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i

Abdullahi ya ce an gudanar da samamen ne ta hannun jami’an ‘yansanda na sashen Gombe yayin wani aikin yau da kullum na fatattakar wuraren da aka tabbatar da ayyukan laifi a yankin.

 

LABARAI MASU NASABA

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

Ya bayyana cewa a ‘yan watannin da suka gabata, rundunar ta kara kaimi wajen kai samame a wuraren da ake zargin yin laifuka a fadin jihar, a wani bangare na kokarinta na rage yawan shan miyagun kwayoyi da laifukan da suka shafi hakan, wadanda hukumomi ke cewa sau da dama su kan zama sanadin tashin hankali da aikata laifuka musamman tsakanin matasa.

 

“Lokacin da barayin suka hango tawagar sintiri na kusantowa, sai suka tsere, suka bar tarin miyagun kwayoyi da wasu haramtattun abubuwa a wurin,” in ji Abdullahi.

 

Mai magana da yawun rundunar ya lissafa abubuwan da aka kwato da suka hada da kwayoyin “Suck and Die,” Tramadol da Diazepam, inda ya ce an kwashe su gaba daya zuwa ofishin ‘yansanda domin ci gaba da bincike da daukar matakan da suka dace.

 

“Dukkan shaidun da aka kwato an tafi da su ofishin ‘yansanda, kuma bincike na ci gaba domin gano da kama wadanda suka tsere,” in ji shi.

 

Kwamishinan ‘yansanda, CP Bello Yahaya, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da samamen bisa gaggawa da kwarewa, tare da tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da jajircewa wajen yaki da laifuka da shan miyagun kwayoyi a Jihar Gombe.

 

“Rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa Gombe ta kasance jiha marar laifi da kuma marar miyagun kwayoyi,” in ji shi.

 

“Muna aikawa da gargadi mai karfi ga duk masu aikata laifuka da su daina duk wani nau’i na aikata laifi ko kuma su fuskanci fushin doka,” in ji CP Yahaya.

 

Ya kuma roki jama’a da su ci gaba da bin doka da oda tare da taimaka wa ‘yansanda da sahihan bayanai da za su taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro.

 

“Muna kira ga al’umma da su rika sanar da ofishin ‘yansanda mafi kusa idan sun ga wani motsi ko aiki da suke shakka domin a dauki mataki cikin gaggawa,” in ji sanarwar.

 

A watan Afrilu, Rundunar ‘Yansandan Jihar Ogun ta gudanar da aikin tsaro na tsawon sa’o’i biyu a Sagamu Interchange bayan samun rahoton wani harin ‘yan fashi da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum a kan hanyar Lagos–Ibadan Expressway.

 

A cewar rundunar, kwamishinan ‘yan sanda Lanre Ogunlowo ne ya jagoranci duba wurin, inda aka gano haramtattun kasuwanin, ‘yan daba da kuma maboyar ‘yan ta’adda a cikin dazukan da ke kusa da wurin.

 

A lokacin aikin tsaron, an kama mutum uku da ake zargi, sannan kuma an kara tsaurara sintiri a yankin domin hana sake kai irin wannan hari a nan gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

October 12, 2025
Gwamna Aliyu Ya Tsige Hakimai 15 Na Sokoto
Tsaro

A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato

October 11, 2025
Next Post
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.