‘Yansanda a Jihar Delta sun kama wani da ake zargin ɗan bindiga ne mai suna Sanusi Abdulahi.
A lokacin da suka kama shi, yana ɗauke da kuɗin Naira miliyan biyar, wanda kuɗin fansa ne da aka biya domin sakin ɗaya daga cikin mutanen da aka sace.
- EU, Turkiyya Da Sauran Ƙasashe Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Buhari
- VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano
Kakakin rundunar, Bright Edafe, ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar.
A cewar Edafe, an kama Abdulahi ne a safiyar ranar 12 ga watan Yuli, 2025, da misalin ƙarfe 6:30 na safe.
‘Yan sanda sun kuma kama wasu mutum huɗu da ake zargi suna cikin tawagar Abdulahi.
Bincike ya nuna cewa su ne ke da hannu a wasu sace-sacen mutane a wurare kamar Ibusa, Ogwashi-Ukwu, Obulu-Okiti, Isele-Ukwu, Isele-Asagba, da kuma sace wata yarinya da ya fa Ogwashi-Ukwu a ranar 9 ga watan Yuli, 2025.
Abdulahi ya jagoranci ‘yansanda zuwa maɓoyarsu a unguwannin Second Deputy da Oko dake Asaba, inda aka kama sauran abokan aikinsa huɗu.
Edafe ya ce har yanzu bincike na gudana.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp