ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

by Sadiq
6 months ago
Kano

Rundunar ‘yansandan Jihar Kano, ta kama matasa 51 da ake zargi da addabar jihar da faɗan daba. 

Haka kuma ta ƙwato makamai masu hatsari da miyagun ƙwayoyi a yayin wani samame da ta kai na tsawon kwana uku a sassa daban-daban na birnin Kano.

  • Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu
  • Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

An gudanar da samamen ne daga ranar Juma’a, 13 ga watan Yuni, zuwa Lahadi, 15 ga watan Yuni.

ADVERTISEMENT

‘Yansanda sun mayar da hankali wuraren da aka fi samun aikata laifi a ƙananan hukumomin Birni, Dala, Gwale, da Tarauni.

Sauran sun haɗa da unguwannin Kofar Mata, Zage, Kurna, Rijiyar Lemo, Dorayi, Hotoro da Sheka.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

DSP Hussaini Abdullahi, Mataimakin Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a madadin Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, a ranar Litinin, 16 ga watan Yuni.

Yawancin waɗanda aka kama matasa ne ‘yan tsakanin shekaru 15 zuwa 39.

Ana zargin su da shiga harkar daba, faɗa a titi da kuma amfani da miyagun ƙwayoyi.

‘Yansanda sun ce wannan samame wani ɓangare ne na ƙoƙarin da suke yi na daƙile daba da dawo da zaman lafiya a birnin Kano.

Kwamishinan ‘Yansandan ya ja kunnen jama’a ka da su riƙa ɗaukar makamai a yayin shagulgulan gargajiya kamar “Gangi”, ko kuma nuna makamai a shafukan sada zumunta kamar TikTok, Facebook, Instagram da X, domin hakan na jawo wa matasa sha’awar shiga ayyukan daba.

Sanarwar ta kuma yi gargaɗi ga iyaye, da kuma masu ƙera makamai cewa duk wanda aka samu yana ɓoye ko taimaka wa ‘yan daba, ko kuma yana ƙera makaman da ake amfani da su wajen tashin hankali, za a gudanar da bincike a kansa tare da gurfanar da shi a gaban kotu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.