• English
  • Business News
Tuesday, June 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

by Sadiq
6 hours ago
in Manyan Labarai
0
‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Kano, ta kama matasa 51 da ake zargi da addabar jihar da faɗan daba. 

Haka kuma ta ƙwato makamai masu hatsari da miyagun ƙwayoyi a yayin wani samame da ta kai na tsawon kwana uku a sassa daban-daban na birnin Kano.

  • Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu
  • Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

An gudanar da samamen ne daga ranar Juma’a, 13 ga watan Yuni, zuwa Lahadi, 15 ga watan Yuni.

‘Yansanda sun mayar da hankali wuraren da aka fi samun aikata laifi a ƙananan hukumomin Birni, Dala, Gwale, da Tarauni.

Sauran sun haɗa da unguwannin Kofar Mata, Zage, Kurna, Rijiyar Lemo, Dorayi, Hotoro da Sheka.

Labarai Masu Nasaba

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

DSP Hussaini Abdullahi, Mataimakin Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a madadin Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, a ranar Litinin, 16 ga watan Yuni.

Yawancin waɗanda aka kama matasa ne ‘yan tsakanin shekaru 15 zuwa 39.

Ana zargin su da shiga harkar daba, faɗa a titi da kuma amfani da miyagun ƙwayoyi.

‘Yansanda sun ce wannan samame wani ɓangare ne na ƙoƙarin da suke yi na daƙile daba da dawo da zaman lafiya a birnin Kano.

Kwamishinan ‘Yansandan ya ja kunnen jama’a ka da su riƙa ɗaukar makamai a yayin shagulgulan gargajiya kamar “Gangi”, ko kuma nuna makamai a shafukan sada zumunta kamar TikTok, Facebook, Instagram da X, domin hakan na jawo wa matasa sha’awar shiga ayyukan daba.

Sanarwar ta kuma yi gargaɗi ga iyaye, da kuma masu ƙera makamai cewa duk wanda aka samu yana ɓoye ko taimaka wa ‘yan daba, ko kuma yana ƙera makaman da ake amfani da su wajen tashin hankali, za a gudanar da bincike a kansa tare da gurfanar da shi a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaFaɗan DabakanoMatasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Next Post

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Related

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran
Kasashen Ketare

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

32 minutes ago
Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna
Manyan Labarai

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

2 hours ago
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

5 hours ago
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Soke Ziyarar Kaduna, Zai Tafi Benuwe Saboda Rikice-Rikice

18 hours ago
Hauhawar Farashi Ya Sauka Zuwa Kashi 22.9 A Watan Mayun 2025
Manyan Labarai

Hauhawar Farashi Ya Sauka Zuwa Kashi 22.9 A Watan Mayun 2025

19 hours ago
Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

1 day ago
Next Post
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

June 17, 2025
Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

June 17, 2025
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

June 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

June 17, 2025
Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

June 16, 2025
Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

June 16, 2025
Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

June 16, 2025
Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

June 16, 2025
Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

June 16, 2025
Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake

Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake

June 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.