• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an rundunar ‘yansandan Jihar Delta sun kama wasu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne, sun kwato wata mota kirar Mercedes Benz GLK da aka sace, da muggan bindigogi da dama da wasu kayayyaki masu daraja.

Wanda ake zargin mai suna Chinedu Eze, an kama shi ne a lokacin da yake kokarin sayar da motar ga wani mai saye da ba a yi tsammani ba.

  • Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu
  • Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

An gudanar da ayyukan ne a tsakanin ranekun 4 zuwa 5 ga Agustan 2025, karkashin jagorancin jami’an ‘yansanda reshen, (DPO) na B Dibision Asaba da Ogwashi-Ukwu, da ke aiki da kungiyoyin ‘yan banga.

Da yake bayyana hakan, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan (PPRO), SP Bright Edafe, ya ce a ranar 5 ga Agusta, jami’an B Dibision Asaba, da ke aiki da sahihan bayanan sirri, sun kama wata mota kirar Mercedes Benz GLK (Lambar Rijista: NZM10AP) a wani wurin ajiye motoci da ke kan titin tsohon mataimakin Gwamna, Asaba.

“Wanda ake zargin mai suna Chinedu Eze, an kama shi ne a lokacin da yake kokarin siyar da motar ga wani mai saye da ba a yi tsammani ba.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Bincike ya nuna cewa ankkwace motar SUB da karfi ne a watan Afrilun 2023 a garin Abakpa da ke Jihar Enugu, inda wasu ‘yan fashi da makami suka harbe mai motar. An sake yi wa motar rajistar zamba a shekarar 2025.

“A wani lamari na daban a ranar 4 ga watan Agusta, da misalin karfe 4:30 na safe, ‘yansanda a Ogwashi-Ukwu sun amsa kira bayan da ‘yan fashi da makami da suka addabi mazauna kan titin Chelsea.

DPO, CSP Okoyomon Israel, ya yi gaggawar tattara rundunarsa mai yaki da laifuka da kuma ‘yan banga zuwa wurin.

“An kama wasu mutane biyu, Thywill Selbin mai shekara na Poly Road, Ogwashi-Ukwu, da Guntim Bako mai shekara 32 na Kwale Junction, bayan yunkurin tserewa da bai yi nasara ba.

“Bindiga guda daya tare da harsashi mai rai daya, bindigar Beretta guda daya mai jigida shida masu rai, harsashin bindiga uku masu rai, babura biyu da aka sace (Daylong, Reg No: SAP 369 BK; Ku link, Reg No: URM 750 KB), wayoyin hannu 25, kwamfyutoci hudu, kwamfutar hannu, kwamfutar hannu, PS4, jakunkuna guda biyar, kayan kida guda biyar, ,” ya bayyana.

Edafe ya ce da dama daga cikin wadanda abin ya shafa sun gano tare da kwato kayansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yansanda
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ɗan Takarar Gwamnan Zamfara, Shinkafi, Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Next Post

An Kama Wakilin Jam’iyya Da Miliyan ₦29 Zai Sayi Ƙuri’a A Kaduna

Related

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

15 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

16 hours ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

1 week ago
‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

1 week ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

1 month ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

1 month ago
Next Post
An Kama Wakilin Jam’iyya Da Miliyan ₦29 Zai Sayi Ƙuri’a A Kaduna

An Kama Wakilin Jam'iyya Da Miliyan ₦29 Zai Sayi Ƙuri'a A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.