• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

by Sulaiman
8 months ago
Abuja

Jami’an rundunar ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja sun ceto wata mata ‘yar shekara 25 mai suna Promise Eze, bayan da wani mutum da ta hadu da shi a wani dandalin sada zumunta na intanet ya daure ta ya bar ta a sume.

Wanda ake zargin da aka bayyana sunansa da Michael Prince amma daga baya ya bayyana sunansa na gaskiya da Emmanuel Okoro, yanzu haka ya tsere, kuma ‘yansanda sun kaddamar da farautarsa domin tabbatar da cafke shi cikin gaggawa.

  • Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
  • Me Ke Kawo Saurin Talaucewa Bayan Kammala Aikin Gwamnati?

Wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan, Josephine Adeh, ta fitar, ta ce ‘yansandan sun samu kiran gaggawa daga wani otal da ke unguwar Wuse a cikin Babban Birnin Tarayya Abuja bayan sun lura da wasu abubuwa da ake zargi a daya daga cikin dakinta.

Adeh ta ce da isowar jami’anta ne suka gano Eze daure a kan wata karamar kujera da bakinta a manne da filasta, kuma tana kwance a kasa a sume.

Ta lura cewa nan take aka garzaya da Eze asibitin gundumar Wuse, inda aka taimaka wajen farfado da ita.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

“Da sauri jami’an ‘yansanda suka isa wurin, inda suka gano wata mata ‘yar shekara 25 mai suna Promise Eze, ‘yar Jihar Ebonyi, daure a wata karamar kujera an rufe bakinta da filasta. An same ta a sume kuma cikin damuwa. Jami’an ‘yan sanda sun dauki matakin gaggawa, inda suka kubutar da ita daga hannun wadanda aka yi garkuwa da su, sannan suka garzaya da ita asibitin gundumar Wuse, inda ta farfado,” in ji sanarwar.

Adeh ta ce binciken farko da aka yi ya nuna cewa Eze ta leka otal din a safiyar ranar 30 ga watan Janairu tare da Okoro, wanda ta hadu da shi ta intanet.

A cewarta, wanda ake zargin ya gabatar da kansa a matsayin ma’aikacin kamfanin mai da ke Jihar Delta.

Adeh ta bayyana cewa tun da farko wanda ake zargin ya gayyaci Eze ta ziyarce shi a Jihar Delta amma ta ki amincewa da hakan amma ta amince ta same shi a Abuja a maimakon haka.

“Bincike na farko ya nuna wani yanayi na yaudara da tashin hankali, ta shiga otal ne kwana daya da ta gabata, a ranar 30 ga watan Janairu, 2025, da misalin karfe 7:00 na safe, tare da wani mutum da ya bayyana sunansa da Emmanuel Okoro daga Jihar Legas.

“Sai dai yayin da ‘yansanda ke mata tambayoyi, matar da aka cutar ta bayyana cewa ta hadu da wanda ake zargin a intanet, inda ya gabatar da kansa ga Michael Prince, inda ya ce shi ma’aikacin kamfanin mai ne da ke Jihar Delta.”

Adeh ta kara da cewa Eze ya ce Okoro ya fid da wuka don yi mata barazana kafin ya daure ta ya manne bakinta a cikin bandakin otal din.

Adeh ta ce kwamishinan ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja, CP Olatunji Disu, ya yi Allah wadai da faruwar lamarin tare da shawartar ‘yanmata kan illar haduwa da baki ta intanet ba tare da taka tsantsan ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Tankar Iskar Gas Ta Fashe, Ta Lalata Motoci Da Shaguna A Neja

Tankar Iskar Gas Ta Fashe, Ta Lalata Motoci Da Shaguna A Neja

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.