Rundunar Ƴansandan Nijeriya ta ƙaryata jita-jitar da ke yawo cewa jirginta mai saukar ungulu yana kai wa ƴan bindiga abinci a dajin Jihar Kogi.
Kakakin rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya ce labarin ba gaskiya ba ne, kuma babu wata shaida da ke tabbatar da hakan.
- ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME
- Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Ya bayyana cewa bidiyon da ke yawo a kafafen sada zumunta na wani aiki ne da jami’an ƴansanda suka gudanar a garin Obajana na jihar Kogi.
A cewar Adejobi, aikin haÉ—in gwiwa ne tsakanin Æ´ansanda, Æ´an banga, da kuma mafarauta, wanda aka yi a ranar Asabar, 10 ga watan Mayu, 2025.
An shigar da jirgin sama a aikin ne domin taimaka wa jami’an tsaro wajen bin sahun ƴan bindiga.
Rundunar ta ce ta gudanar da aikin bisa ƙa’ida da bin doka, kuma tana Allah-wadai da masu yaɗa ƙarya da nufin ɓata mata suna.
Ƴansandan sun jaddada cewa za su ci gaba da aikinsu na yaƙi da laifi da bin doka da ƙwarewa a duk faɗin ƙasar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp