• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-Yanzu: Kotun Daukaka Kara Ta Sallami Nnamdi Kanu, Ta Kalubalanci Hukuncin Babbar Kotu 

by Sadiq
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Yanzu-Yanzu: Kotun Daukaka Kara Ta Sallami Nnamdi Kanu, Ta Kalubalanci Hukuncin Babbar Kotu 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta sallami shugaban masu rajin fafutukar kafa kasar Biyafara, Nnamdi Kanu.

Gwamnatin Tarayya ta gurfanar da Kanu a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja bisa tuhume-tuhume 15 da suka shafi cin amanar kasa da ta’addanci, laifuffukan da ake zarginsa da aikatawa a yayin yakin neman zabensa.

  • An Yi Wa Manoma 5 Yankan Rago A Wani Sabon Rikici A Benuwe
  • 2023: Kuri’a Miliyan 95 Ce Za Ta Bayyana Wanda Zai Gaji Buhari – INEC

Wani kwamitin mutane uku da kotun daukaka kara, ya ce babbar kotun tarayya ba ta da hurumin yi masa shari’a bisa la’akari da yadda aka tsare shi da kuma yadda aka yi da shi wanda ya sabawa ka’ida.

Kotun ta ce tuhume-tuhume 15 da ake tuhumar Kanu ba a bayyana, kwanan wata, lokaci da kuma yanayin laifukan da ake zarginsa da aikatawa ba kafin a mika shi zuwa Nijeriya, wanda ya sabawa yarjejeniyar kasa da kasa.

Kotun ta ci gaba da cewa gwamnatin tarayya ta kasa bayyana inda aka kama Nnamdi Kanu duk da zarge-zargen da ake yi masa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

An Zarge Shi Da Laifin Cin Amanar Kasa 

Mista Kanu ya sha yin kira da a balle wani yanki na kudancin Nijeriya domin kafa Jamhuriyar Biyafara.

A watan Oktoban 2015, hukumomin Nijeriya sun kama shi kan tuhume-tuhume 11 da suka hada da “ta’addanci, cin amanar kasa, jagorantar al’umma ba bisa ka’ida ba, buga labaran batanci, mallakar makamai ba bisa ka’ida ba da shigo da kaya ba bisa ka’ida ba, da sauransu.

“An bayar da belinsa ne a watan Afrilun 2017 saboda dalilai da suka shafi rashin lafiya.

“Sai dai Mista Kanu ya tsere daga kasar a watan Satumban 2017 bayan da sojoji suka mamaye gidansa da ke Afara-Ukwu, kusa da Umuahia a Jihar Abiya.

“Daga nan ne aka gan shi a Isra’ila, daga baya kuma ya ci gaba da tara magoya bayansa a Nijeriya don yin amfani da tashin hankali wajen samun ballewa.

“An zarge shi da laifin yin zagon kasa da ya hada da tada tarzoma ta hanyar talabijin da rediyo da watsa shirye-shirye ta yanar gizo a kan Nijeriya da jihohi da hukumomin Nijeriya,” in ji Ministan Shari’a, Abubakar Malami bayan an sake kama Kanu tare da dawo da shi Nijeriya a watan Yuni 2021.

“An kuma zargi Kanu da haddasa tashin hankali musamman a yankin Kudu maso Gabashin Nijeriya wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyin fararen hula, sojoji, jami’an ‘yansanda da lalata cibiyoyin farar hula da hukumomi.”

Mista Kanu ya musanta aikata laifikan da ake tuhumarsa da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BiyafaraCin AmanaHukunciKanuKotuZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Wa Manoma 5 Yankan Rago A Wani Sabon Rikici A Benuwe

Next Post

Ya Kamata Amurka Ta Koyi Darasi Daga Yakin Harajin Da Bai Yi Nasara Ba Kan Sin

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

4 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

9 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

11 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

14 hours ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

18 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

19 hours ago
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Koyi Darasi Daga Yakin Harajin Da Bai Yi Nasara Ba Kan Sin

Ya Kamata Amurka Ta Koyi Darasi Daga Yakin Harajin Da Bai Yi Nasara Ba Kan Sin

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.