ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-Yanzu: Kotun Daukaka Kara Ta Sallami Nnamdi Kanu, Ta Kalubalanci Hukuncin Babbar Kotu 

by Sadiq
4 years ago
Kanu

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta sallami shugaban masu rajin fafutukar kafa kasar Biyafara, Nnamdi Kanu.

Gwamnatin Tarayya ta gurfanar da Kanu a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja bisa tuhume-tuhume 15 da suka shafi cin amanar kasa da ta’addanci, laifuffukan da ake zarginsa da aikatawa a yayin yakin neman zabensa.

  • An Yi Wa Manoma 5 Yankan Rago A Wani Sabon Rikici A Benuwe
  • 2023: Kuri’a Miliyan 95 Ce Za Ta Bayyana Wanda Zai Gaji Buhari – INEC

Wani kwamitin mutane uku da kotun daukaka kara, ya ce babbar kotun tarayya ba ta da hurumin yi masa shari’a bisa la’akari da yadda aka tsare shi da kuma yadda aka yi da shi wanda ya sabawa ka’ida.

ADVERTISEMENT

Kotun ta ce tuhume-tuhume 15 da ake tuhumar Kanu ba a bayyana, kwanan wata, lokaci da kuma yanayin laifukan da ake zarginsa da aikatawa ba kafin a mika shi zuwa Nijeriya, wanda ya sabawa yarjejeniyar kasa da kasa.

Kotun ta ci gaba da cewa gwamnatin tarayya ta kasa bayyana inda aka kama Nnamdi Kanu duk da zarge-zargen da ake yi masa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

An Zarge Shi Da Laifin Cin Amanar Kasa 

Mista Kanu ya sha yin kira da a balle wani yanki na kudancin Nijeriya domin kafa Jamhuriyar Biyafara.

A watan Oktoban 2015, hukumomin Nijeriya sun kama shi kan tuhume-tuhume 11 da suka hada da “ta’addanci, cin amanar kasa, jagorantar al’umma ba bisa ka’ida ba, buga labaran batanci, mallakar makamai ba bisa ka’ida ba da shigo da kaya ba bisa ka’ida ba, da sauransu.

“An bayar da belinsa ne a watan Afrilun 2017 saboda dalilai da suka shafi rashin lafiya.

“Sai dai Mista Kanu ya tsere daga kasar a watan Satumban 2017 bayan da sojoji suka mamaye gidansa da ke Afara-Ukwu, kusa da Umuahia a Jihar Abiya.

“Daga nan ne aka gan shi a Isra’ila, daga baya kuma ya ci gaba da tara magoya bayansa a Nijeriya don yin amfani da tashin hankali wajen samun ballewa.

“An zarge shi da laifin yin zagon kasa da ya hada da tada tarzoma ta hanyar talabijin da rediyo da watsa shirye-shirye ta yanar gizo a kan Nijeriya da jihohi da hukumomin Nijeriya,” in ji Ministan Shari’a, Abubakar Malami bayan an sake kama Kanu tare da dawo da shi Nijeriya a watan Yuni 2021.

“An kuma zargi Kanu da haddasa tashin hankali musamman a yankin Kudu maso Gabashin Nijeriya wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyin fararen hula, sojoji, jami’an ‘yansanda da lalata cibiyoyin farar hula da hukumomi.”

Mista Kanu ya musanta aikata laifikan da ake tuhumarsa da su.

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Koyi Darasi Daga Yakin Harajin Da Bai Yi Nasara Ba Kan Sin

Ya Kamata Amurka Ta Koyi Darasi Daga Yakin Harajin Da Bai Yi Nasara Ba Kan Sin

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.