ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-Yanzu: Kotun Daukaka Kara Ta Sallami Nnamdi Kanu, Ta Kalubalanci Hukuncin Babbar Kotu 

by Sadiq
4 years ago
Kanu

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta sallami shugaban masu rajin fafutukar kafa kasar Biyafara, Nnamdi Kanu.

Gwamnatin Tarayya ta gurfanar da Kanu a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja bisa tuhume-tuhume 15 da suka shafi cin amanar kasa da ta’addanci, laifuffukan da ake zarginsa da aikatawa a yayin yakin neman zabensa.

  • An Yi Wa Manoma 5 Yankan Rago A Wani Sabon Rikici A Benuwe
  • 2023: Kuri’a Miliyan 95 Ce Za Ta Bayyana Wanda Zai Gaji Buhari – INEC

Wani kwamitin mutane uku da kotun daukaka kara, ya ce babbar kotun tarayya ba ta da hurumin yi masa shari’a bisa la’akari da yadda aka tsare shi da kuma yadda aka yi da shi wanda ya sabawa ka’ida.

ADVERTISEMENT

Kotun ta ce tuhume-tuhume 15 da ake tuhumar Kanu ba a bayyana, kwanan wata, lokaci da kuma yanayin laifukan da ake zarginsa da aikatawa ba kafin a mika shi zuwa Nijeriya, wanda ya sabawa yarjejeniyar kasa da kasa.

Kotun ta ci gaba da cewa gwamnatin tarayya ta kasa bayyana inda aka kama Nnamdi Kanu duk da zarge-zargen da ake yi masa.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

An Zarge Shi Da Laifin Cin Amanar Kasa 

Mista Kanu ya sha yin kira da a balle wani yanki na kudancin Nijeriya domin kafa Jamhuriyar Biyafara.

A watan Oktoban 2015, hukumomin Nijeriya sun kama shi kan tuhume-tuhume 11 da suka hada da “ta’addanci, cin amanar kasa, jagorantar al’umma ba bisa ka’ida ba, buga labaran batanci, mallakar makamai ba bisa ka’ida ba da shigo da kaya ba bisa ka’ida ba, da sauransu.

“An bayar da belinsa ne a watan Afrilun 2017 saboda dalilai da suka shafi rashin lafiya.

“Sai dai Mista Kanu ya tsere daga kasar a watan Satumban 2017 bayan da sojoji suka mamaye gidansa da ke Afara-Ukwu, kusa da Umuahia a Jihar Abiya.

“Daga nan ne aka gan shi a Isra’ila, daga baya kuma ya ci gaba da tara magoya bayansa a Nijeriya don yin amfani da tashin hankali wajen samun ballewa.

“An zarge shi da laifin yin zagon kasa da ya hada da tada tarzoma ta hanyar talabijin da rediyo da watsa shirye-shirye ta yanar gizo a kan Nijeriya da jihohi da hukumomin Nijeriya,” in ji Ministan Shari’a, Abubakar Malami bayan an sake kama Kanu tare da dawo da shi Nijeriya a watan Yuni 2021.

“An kuma zargi Kanu da haddasa tashin hankali musamman a yankin Kudu maso Gabashin Nijeriya wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyin fararen hula, sojoji, jami’an ‘yansanda da lalata cibiyoyin farar hula da hukumomi.”

Mista Kanu ya musanta aikata laifikan da ake tuhumarsa da su.

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Koyi Darasi Daga Yakin Harajin Da Bai Yi Nasara Ba Kan Sin

Ya Kamata Amurka Ta Koyi Darasi Daga Yakin Harajin Da Bai Yi Nasara Ba Kan Sin

LABARAI MASU NASABA

Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.