• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaron Da Ya Yi Bulaguro Zuwa Waje Zai Koma Gida

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yaron Da Ya Yi Bulaguro Zuwa Waje Zai Koma Gida

Ci'en pagoda architecture with Sun Moon Lake

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin nan, maganar Taiwan ta sake janyo hankalin mutanen duniya, sakamakon yadda wata babbar jami’ar kasar Amurka ta kai ziyara a yankin Taiwan na kasar Sin, duk da rashin amincewa da gargadi da gwamnatin kasar Sin ta yi, lamarin da ya tilasta wa Sin daukar wasu matakai, ciki har da atisayen soja a kewayen tsibirin Taiwan.

Duk lokacin da aka ambaci Taiwan ya kan sa ni tunawa da wani batun da ya faru a baya: Wata rana, na je ajiye kudi a wani banki a birnin Ikko na Najeriya. Ina jira a zo kaina, sai wani ma’aikacin banki ya taimaye ni, “Me ya sa kasar Sin ba ta yarda da ‘yancin kan Taiwan ba?”.

  • Kasar Sin Na Gudanar Da Atisayen Soji A Rawayen Teku Da Tekun Bohai

Maimakon na amsa tambayarsa, sai ni ma na yi masa tambaya: “Me ya sa Najeriya ba ta yarda da ‘yancin kan Biafra ba?” Ma’aikacin ya rasa abin da zai fada.
Wasu kafofin yada labaru da ‘yan siyasa na kasashen yamma suna son kwatanta Taiwan da Ukraine, amma hakika akwai bambanci tsakaninsu.

Ukraine wata kasa ce, yayin da Taiwan wani yanki ne na kasar Sin. Kasar Sin ba za ta yarda da ‘yancin kan Taiwan ba, kamar yadda ita ma gwamnatin Najeriya ba za ta taba amincewa da ballewar yankin kudu maso gabashin kasar, da kafuwar “jamhuriyar Biafra” ba.

Duk wanda ya ke karanta labarun abubuwan dake faruwa a sassan duniya, tabbas ya taba jin manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya. Ma’anar wannan manufa ita ce: Kasar Sin daya ce tak a duniyarmu, Taiwan wani yanki ne na kasar Sin da ba za a iya balle shi ba, kana gwamnatin jamhuriyar jama’ar kasar Sin, ita ce halaltacciyar gwamnati daya tak da take wakiltar daukacin al’ummun Sin.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Wannan manufa ita ce tushen kulla huldar diplomasiya tare da kasar Sin, kana wata babbar ka’ida ce da Majalisar Dinkin Duniya da gamayyar kasa da kasa suke amincewa da ita.

Saboda dukkan kasashen da suka kulla huldar diplomasiya tare da kasar Sin sun yin alkawarin girmama manufar kasancewar kasar Sin daya tak, sa’an nan galibin kasashen duniya sun riga sun kulla hulda da Sin. Don haka, idan kowace kasa ta iya cika alkawarin da ta yi, to, ba za a samu maganar Taiwan ba.

Amma abin takaici shi ne, akwai kasar da ta yi amai ta lashe kan wannan manufa.
Babban dalilin da ya haddasa maganar Taiwan shi ne kasar Amurka. Da ma a shekarar 1949, Sinawa sun kawo karshen yakin basasa na kasar na shekaru 3, tare da kafa jamhuriyar jama’ar kasar Sin.

A lokacin, wasu sojoji da jami’ai na jam’iyyar Kuomintang sun gudu zuwa tsibirin Taiwan na kasar, inda suka mallaki tsibirin bisa goyon bayan gwamnatin kasar Amurka.

Daga bisani, Amurka ta fara yin amfani da maganar Taiwan wajen neman shawo kan kasar Sin: Idan tana neman samun goyon bayan kasar Sin, sai ta dan nisanta kanta da bangaren Taiwan.

Amma idan tana so ta matsawa kasar Sin lamba, to, sai ta bijiro da maganar baiwa yankin Taiwan tallafin makamai, da nuna goyon baya ga masu neman ‘yancin kan Taiwan a asirce, ko kuma sanya wasu manyan jami’anta kai ziyara yankin Taiwan, da dai sauransu.

Sanin kowa ne cewa, Amurka ta kwashe fiye da shekaru 70 tana yin haka, shin za ta iya kiyaye yanayin a wannan zamanin da muke ciki? Bayan da Nancy Pelosi, babbar jami’a mai matsayi na uku a gwamnatin kasar Amurka, ta ziyarci yankin Taiwan a wannan karo, rundunar sojojin kasar Sin ta kaddamar da babban atisayen soja a kewayen Taiwan, wanda ba a taba ganin irinsa ba a baya.

Hakan ya shaida karfin kasar a fannin dinke kasa ta matakan soja. Sai dai za ta ci gaba da neman dinkuwar kasa waje guda ta hanyar lumana. Sinawa suna da cikakken imani kan makomar lamarin.

A ganinsu, abin da ya faru sakamakon yadda al’ummar kasar ba su da karfi a baya, za a iya daidaita shi, bayan da kasar ta samu ci gaba, da farfadowar al’ummarta.

A ganin Sinawa, yankin Taiwan tamkar wani yaro da ya bar gida, ya tafi bulaguro a waje, kuma tabbas wata rana zai koma gida. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Falakin Karaye Ya Nemi Al’umma Su Rungumi Yi Wa Kasa Addu’a

Next Post

An Saki Tsofaffin Gwamnoni, Dariye Da Nyame Daga Gidan Yarin Kuje

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

3 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

5 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

5 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

9 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

11 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

11 hours ago
Next Post
An Saki Tsofaffin Gwamnoni, Dariye Da Nyame Daga Gidan Yarin Kuje

An Saki Tsofaffin Gwamnoni, Dariye Da Nyame Daga Gidan Yarin Kuje

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.