ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaron Da Ya Yi Bulaguro Zuwa Waje Zai Koma Gida

by CMG Hausa
3 years ago
Ci'en pagoda architecture with Sun Moon Lake

Ci'en pagoda architecture with Sun Moon Lake

A kwanakin nan, maganar Taiwan ta sake janyo hankalin mutanen duniya, sakamakon yadda wata babbar jami’ar kasar Amurka ta kai ziyara a yankin Taiwan na kasar Sin, duk da rashin amincewa da gargadi da gwamnatin kasar Sin ta yi, lamarin da ya tilasta wa Sin daukar wasu matakai, ciki har da atisayen soja a kewayen tsibirin Taiwan.

Duk lokacin da aka ambaci Taiwan ya kan sa ni tunawa da wani batun da ya faru a baya: Wata rana, na je ajiye kudi a wani banki a birnin Ikko na Najeriya. Ina jira a zo kaina, sai wani ma’aikacin banki ya taimaye ni, “Me ya sa kasar Sin ba ta yarda da ‘yancin kan Taiwan ba?”.

  • Kasar Sin Na Gudanar Da Atisayen Soji A Rawayen Teku Da Tekun Bohai

Maimakon na amsa tambayarsa, sai ni ma na yi masa tambaya: “Me ya sa Najeriya ba ta yarda da ‘yancin kan Biafra ba?” Ma’aikacin ya rasa abin da zai fada.
Wasu kafofin yada labaru da ‘yan siyasa na kasashen yamma suna son kwatanta Taiwan da Ukraine, amma hakika akwai bambanci tsakaninsu.

ADVERTISEMENT

Ukraine wata kasa ce, yayin da Taiwan wani yanki ne na kasar Sin. Kasar Sin ba za ta yarda da ‘yancin kan Taiwan ba, kamar yadda ita ma gwamnatin Najeriya ba za ta taba amincewa da ballewar yankin kudu maso gabashin kasar, da kafuwar “jamhuriyar Biafra” ba.

Duk wanda ya ke karanta labarun abubuwan dake faruwa a sassan duniya, tabbas ya taba jin manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya. Ma’anar wannan manufa ita ce: Kasar Sin daya ce tak a duniyarmu, Taiwan wani yanki ne na kasar Sin da ba za a iya balle shi ba, kana gwamnatin jamhuriyar jama’ar kasar Sin, ita ce halaltacciyar gwamnati daya tak da take wakiltar daukacin al’ummun Sin.

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Wannan manufa ita ce tushen kulla huldar diplomasiya tare da kasar Sin, kana wata babbar ka’ida ce da Majalisar Dinkin Duniya da gamayyar kasa da kasa suke amincewa da ita.

Saboda dukkan kasashen da suka kulla huldar diplomasiya tare da kasar Sin sun yin alkawarin girmama manufar kasancewar kasar Sin daya tak, sa’an nan galibin kasashen duniya sun riga sun kulla hulda da Sin. Don haka, idan kowace kasa ta iya cika alkawarin da ta yi, to, ba za a samu maganar Taiwan ba.

Amma abin takaici shi ne, akwai kasar da ta yi amai ta lashe kan wannan manufa.
Babban dalilin da ya haddasa maganar Taiwan shi ne kasar Amurka. Da ma a shekarar 1949, Sinawa sun kawo karshen yakin basasa na kasar na shekaru 3, tare da kafa jamhuriyar jama’ar kasar Sin.

A lokacin, wasu sojoji da jami’ai na jam’iyyar Kuomintang sun gudu zuwa tsibirin Taiwan na kasar, inda suka mallaki tsibirin bisa goyon bayan gwamnatin kasar Amurka.

Daga bisani, Amurka ta fara yin amfani da maganar Taiwan wajen neman shawo kan kasar Sin: Idan tana neman samun goyon bayan kasar Sin, sai ta dan nisanta kanta da bangaren Taiwan.

Amma idan tana so ta matsawa kasar Sin lamba, to, sai ta bijiro da maganar baiwa yankin Taiwan tallafin makamai, da nuna goyon baya ga masu neman ‘yancin kan Taiwan a asirce, ko kuma sanya wasu manyan jami’anta kai ziyara yankin Taiwan, da dai sauransu.

Sanin kowa ne cewa, Amurka ta kwashe fiye da shekaru 70 tana yin haka, shin za ta iya kiyaye yanayin a wannan zamanin da muke ciki? Bayan da Nancy Pelosi, babbar jami’a mai matsayi na uku a gwamnatin kasar Amurka, ta ziyarci yankin Taiwan a wannan karo, rundunar sojojin kasar Sin ta kaddamar da babban atisayen soja a kewayen Taiwan, wanda ba a taba ganin irinsa ba a baya.

Hakan ya shaida karfin kasar a fannin dinke kasa ta matakan soja. Sai dai za ta ci gaba da neman dinkuwar kasa waje guda ta hanyar lumana. Sinawa suna da cikakken imani kan makomar lamarin.

A ganinsu, abin da ya faru sakamakon yadda al’ummar kasar ba su da karfi a baya, za a iya daidaita shi, bayan da kasar ta samu ci gaba, da farfadowar al’ummarta.

A ganin Sinawa, yankin Taiwan tamkar wani yaro da ya bar gida, ya tafi bulaguro a waje, kuma tabbas wata rana zai koma gida. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan
Daga Birnin Sin

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci
Daga Birnin Sin

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Next Post
An Saki Tsofaffin Gwamnoni, Dariye Da Nyame Daga Gidan Yarin Kuje

An Saki Tsofaffin Gwamnoni, Dariye Da Nyame Daga Gidan Yarin Kuje

LABARAI MASU NASABA

DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.