• English
  • Business News
Saturday, August 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Ne Za A Ga Bayan Hare-haren Bindiga A Amurka?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yaushe Ne Za A Ga Bayan Hare-haren Bindiga A Amurka?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Duk lokacin da na ga an sa hannu cikin jaka, na kan ji tsoro”, furuci ke nan na Osadolor Hernandez, wata daliba a jami’ar Chicago ta kasar Amurka, wadda ta ce, “Har ma ina tunanin ko zan haihu lokacin da na girma, sabo da ba na son ganin yara na suna fuskantar barazanar hare-haren bindiga da ka iya afka musu ba zata, abin da ke sa ni jin tsoro a rayuwata ta kowace rana.” Kalaman nata a hakika ya bayyana yanayin da Amurkawa da yawa ke ciki a halin yanzu.

A jiya ma an kai harin bindiga a wata cibiyar kasuwanci da ke bayan birnin Dallas na jihar Texas ta kasar Amurka, harin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 9, ciki har da yara. A wannan rana kuma, an ji harbin bindiga a unguwar Tacony ta birnin Philadelphia, lamarin da ya hallaka mutane biyu tare da jikkata wani.

  • Kasashen Sin Da Afghanistan Da Pakistan Sun Sha Alwashin Karfafa Hadin Gwiwar Inganta Tsaro

In an duba, kusan kowace rana irin wadannan hare-haren bindiga na faruwa a Amurka. A baya baya nan, a ranar 5 ga wata, wani dan bindiga ya harbe wata mace har lahira, tare da ji wa wani rauni a wani filin ajiye motoci da ke Annapolis na jihar Maryland ta kasar Amurka, kafin daga bisani dan bindigar ya kashe kansa.

Sai kuma a ranar 4 ga wata, wasu mutane 4 sun halaka sakamakon harin bindiga da ya faru a kauyen Moultrie da ke kudancin jihar Georgia. A ranar 3 ga wata kuma, an kai harin bindiga ga wani asibitin da ke birnin Atlanta, lamarin da ya halaka wata ma’aikaciyar lafiya, tare da jikkata wasu mutane 4……

Gwamnatin Amurka ta sha suka daga gida da ma waje sakamakon matsalar hare haren bindiga da ke ci wa kasar tuwo a kwarya.

Labarai Masu Nasaba

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Sakamakon matsin da gwamnati take fuskanta, a watan Yunin bara, Shugaban kasar Joe Biden ya sa hannu a kan wani shirin doka na kayyade bindigogi, sai dai abin takaici, yau kusan shekara guda ke nan, amma ko kadan ba a ga alamar kyautatuwar yanayin da ake ciki ba.

Alkaluman da shafin yanar gizo dake bayani game da matsalar harbin bindiga mai suna “Gun Violence Archive” ya fitar sun shaida cewa, a farkon watannin hudu na bana, mutane kusan dubu 14 sun mutu sakamakon hare-haren bindiga a Amurka, adadin da ya kai kimanin 115 a kowace rana ke nan. Sabo da rashin niyyar daidaita ainihin abubuwan da ke haifar da matsalar bindiga, ya sa shirin dokar ya kasa warware matsalar da ake fuskanta.

Tsohon shugaban kasar Amurka Franklin Roosevelt ya taba bayyana cewa, daya daga cikin ‘yancin dan Adam shi ne “’yanci na rashin jin tsoro”. To, amma kasar da ko rayukan jama’arta ta kasa karewa, ina ake zancenta game da ‘yanci da ma hakkin dan Adam?

Domin moriyar wasu gungun mutane, al’ummar Amurka na fama da munanan hasarorin rayuka. Ko yaushe ne za a ga bayan hare-haren bindiga a Amurka? (Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Yi Duk Abin Da Ya Dace Wajen Magance Matsalolin Nijeriya – Shagalinku

Next Post

Lardin Hunan Ya Samu Tagomashin Cinikayyar Waje Tsakanin Sa Da Kasashen Afirka A Rubu’in Farkon Bana

Related

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure
Daga Birnin Sin

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

4 hours ago
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”
Daga Birnin Sin

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

5 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

6 hours ago
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani
Daga Birnin Sin

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

7 hours ago
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

8 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Ya Kamata Japan Ta Martaba Tarihi
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Ya Kamata Japan Ta Martaba Tarihi

9 hours ago
Next Post
Lardin Hunan Ya Samu Tagomashin Cinikayyar Waje Tsakanin Sa Da Kasashen Afirka A Rubu’in Farkon Bana

Lardin Hunan Ya Samu Tagomashin Cinikayyar Waje Tsakanin Sa Da Kasashen Afirka A Rubu’in Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

August 15, 2025
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

August 15, 2025
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

August 15, 2025
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

August 15, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

August 15, 2025
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

August 15, 2025
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

August 15, 2025
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

August 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.