ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Ne Za A Ga Bayan Hare-haren Bindiga A Amurka?

by CMG Hausa
3 years ago
Bindiga

“Duk lokacin da na ga an sa hannu cikin jaka, na kan ji tsoro”, furuci ke nan na Osadolor Hernandez, wata daliba a jami’ar Chicago ta kasar Amurka, wadda ta ce, “Har ma ina tunanin ko zan haihu lokacin da na girma, sabo da ba na son ganin yara na suna fuskantar barazanar hare-haren bindiga da ka iya afka musu ba zata, abin da ke sa ni jin tsoro a rayuwata ta kowace rana.” Kalaman nata a hakika ya bayyana yanayin da Amurkawa da yawa ke ciki a halin yanzu.

A jiya ma an kai harin bindiga a wata cibiyar kasuwanci da ke bayan birnin Dallas na jihar Texas ta kasar Amurka, harin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 9, ciki har da yara. A wannan rana kuma, an ji harbin bindiga a unguwar Tacony ta birnin Philadelphia, lamarin da ya hallaka mutane biyu tare da jikkata wani.

  • Kasashen Sin Da Afghanistan Da Pakistan Sun Sha Alwashin Karfafa Hadin Gwiwar Inganta Tsaro

In an duba, kusan kowace rana irin wadannan hare-haren bindiga na faruwa a Amurka. A baya baya nan, a ranar 5 ga wata, wani dan bindiga ya harbe wata mace har lahira, tare da ji wa wani rauni a wani filin ajiye motoci da ke Annapolis na jihar Maryland ta kasar Amurka, kafin daga bisani dan bindigar ya kashe kansa.

ADVERTISEMENT

Sai kuma a ranar 4 ga wata, wasu mutane 4 sun halaka sakamakon harin bindiga da ya faru a kauyen Moultrie da ke kudancin jihar Georgia. A ranar 3 ga wata kuma, an kai harin bindiga ga wani asibitin da ke birnin Atlanta, lamarin da ya halaka wata ma’aikaciyar lafiya, tare da jikkata wasu mutane 4……

Gwamnatin Amurka ta sha suka daga gida da ma waje sakamakon matsalar hare haren bindiga da ke ci wa kasar tuwo a kwarya.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Sakamakon matsin da gwamnati take fuskanta, a watan Yunin bara, Shugaban kasar Joe Biden ya sa hannu a kan wani shirin doka na kayyade bindigogi, sai dai abin takaici, yau kusan shekara guda ke nan, amma ko kadan ba a ga alamar kyautatuwar yanayin da ake ciki ba.

Alkaluman da shafin yanar gizo dake bayani game da matsalar harbin bindiga mai suna “Gun Violence Archive” ya fitar sun shaida cewa, a farkon watannin hudu na bana, mutane kusan dubu 14 sun mutu sakamakon hare-haren bindiga a Amurka, adadin da ya kai kimanin 115 a kowace rana ke nan. Sabo da rashin niyyar daidaita ainihin abubuwan da ke haifar da matsalar bindiga, ya sa shirin dokar ya kasa warware matsalar da ake fuskanta.

Tsohon shugaban kasar Amurka Franklin Roosevelt ya taba bayyana cewa, daya daga cikin ‘yancin dan Adam shi ne “’yanci na rashin jin tsoro”. To, amma kasar da ko rayukan jama’arta ta kasa karewa, ina ake zancenta game da ‘yanci da ma hakkin dan Adam?

Domin moriyar wasu gungun mutane, al’ummar Amurka na fama da munanan hasarorin rayuka. Ko yaushe ne za a ga bayan hare-haren bindiga a Amurka? (Mai Zane:Mustapha Bulama)

Bindiga
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Lardin Hunan Ya Samu Tagomashin Cinikayyar Waje Tsakanin Sa Da Kasashen Afirka A Rubu’in Farkon Bana

Lardin Hunan Ya Samu Tagomashin Cinikayyar Waje Tsakanin Sa Da Kasashen Afirka A Rubu’in Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.