• English
  • Business News
Friday, October 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

by Mairo Muhammad Mudi
1 month ago
in Bakon Marubuci
0
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ‘yan makwannin da suka gabata, Nijeriya ta sake samun karuwa daga kwallon kafa zuwa kwallon Kwando, har ma da fagen ilimi a ketare; ‘yan matan Nijeriya sun yi nasara a duniya.

A kasar da galibi labarai marasa dadi suka fi yawa, wadannan nasarori uku sun zo ne a jere tare da tunatar da mu cewa; idan akwai dama da karfafa gwiwa, ‘yan matanmu za su iya samun kowace irin nasara a duniya.

  • CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Da farko dai, Super Falcons sun sake kafa tarihi ta hanyar lashe Kofin Mata na Afirka (WAFCON) na 2024 a Kasar Morocco. Bayan haka, D’Tigress, ‘yan kwallon kwando mata na Nijeriya, sun lashe Kofin AfroBasket na FIBA a karo na biyar a jere, lallai abin alfahari ne sosai.

Shugaban kasa ya nuna farin cikinsa ga wadannan nasarori ta hanyar ba su kyautar kudi har Dala100,000 ga kowace ‘yar wasa, gidaje da kuma kambun girmamawa ta kasa (OON). Babu shakka, wannan mataki ne da ya dace; sannan kuma abin a jinjina masa.

Sai kuma, wata nasara ta ban mamaki mai kuma matukar inganci, wanda ake zaton wuta a makera; kwatsam kuma sai ga ta a masaka.

Labarai Masu Nasaba

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

Me Ake Nufi Da Ado? 

‘Yan mata uku daga Jihar Yobe ta Arewa, Fatima Adamu, Falmata Bukar da Aisha Usman; sun wakilci Nijeriya a wata gasa ta Turanci da aka gudanar London, inda suka doke kasashe 69 da suka shiga gasar daga sassan fadin duniya. Ko shakka babu, wannan ba karamin abin alfahari ba ne a ce; daga yankin da galibi ake gani a matsayin guda cikin wadanda suka samu koma baya a fannin ilimi ga kuma talauci, amma wadannan ‘yan mata suka yi irin wannan bazata, ta hanyar lashe wannan gasa.

To sai dai, tambayar da ke ci wa mutane tuwo a kwarya ita ce; me yasa aka bi su da shiru da kuma ko in kula?

Me yasa aka yi wa Super Falcons da D’Tigress kyakkyawar kyauta, amma kuma aka bar ‘yan matan Yobe da sakon taya murna kawai daga fadar shugaban kasa? Ina kyautar girmamawa, ina kudi, ina gidaje, ina daukaka da su ma suka cancanta su samu?

Bari na fito a mutum, wannan ba kokari ne na rage kimar wadanda suka yi fice a fannin wasanni ba. Sun cancanci lambar yabo da suka samu, amma wannan yana kawo wasuwasi ga zukatan wasu, me yasa muke girmama shahara watanni fiye da hazaka a ilimi?

Tsawon shekaru, ana ba da muhimman kyaututtuka ga ‘yan wasa, mawaka da shahararrun mutane, yayin da masu hazaka a fannin ilimi da fasaha ke kasancewa a gefe.

Kamfanin MTN na Nijeriya, sun bayar da Naira miliyan 150 ga Super Falcons, amma har yanzu babu ko kwatankwacin haka ga ‘yan matan Yobe. Ina Kamfanin MTN, Glo, Dangote, BUA da sauran manyan kamfanoni?

Ko saboda daga Yobe suka fito ne, yankin da ya sha fama da rikice-rikicen Boko Haram da koma baya? Ko saboda nasarar ba ta dauki hankalin mutanen kudu a kafafen sada zumunta ba?

Abin da ya fi damun mutane shi ne, shugaban kasa ya san da nasarar, domin kuwa ya tura sakon taya su murna kadai. To, me ya hana a yi musu goma sha biyu ta arziki su ma? Wannan ya kara cusa shakku a zukatan jama’ar Arewa: Shin, shugaban kasa ya fi damuwa da ci gaban Kudu ne kadai ko kuwa?

Mutane da dama a Arewa, sun fara korafi game da yadda ake yi musu rikon sakainar-kashi bayan sun ba da goyon baya mai karfi a zaben shugaban kasa fiye da yankin da ya damu da su a yanzu. Haka zalika, abin takaicin shi ne; yadda manya-manyan jigajigan gwamnati daga Arewa suka yi shiru, watakila saboda kariyar kujerunsu, amma wannan shirun ka iya haifar da rashin yarda ga shugaban kasa, saboda haka; ya kamata su gane cewa, ba taimakon sa suke yi ba.

A wannan gaba, dole ne mu yaba wa Gwamnan Yobe, Alhaji Mai Mala Buni, wanda bai jira fadar shugaban kasa ba, ya karbi ‘yan matan; wanda tun farko shi ne ya dauki nauyinsu, ya kuma girmama su, ya nuna yana alfahari da su, ya kuma yi alkawarin tallafa musu. Wannan shi ne irin shugabancin da ake bukata.

Amma ya kamata a fahimci cewa, wannan nasara ba ta Jihar Yobe ba ce ita kadai, nasara ce ta Nijeriya baki-daya.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana da damar gyara wannan kuskure ta hanyar bai wa wadannan ‘yan mata irin girmamawar da suka cancanta a ba su. Wannan zai isar da sako mai karfi ga iyayen Arewa:

’Ya’yanku mata, suna da hazakar da Nijeriya ke alfahari da ita. Wannan zai sa yara yin tururuwa zuwa makaranta.

Haka kuma, zai dawo da martabar ilimi a kasa da yawan samun daukaka a fannin wasanni da shahara fiye da basira da ilimi.

Saboda haka, shugaban kasa, har yanzu muna jiran mataki mai kyau a kan wadannan ‘yan mata na Yobe.

Fatima, Falmata da Aisha, sun yi wa Nijeriya hidimar da za a yi alfahari da su. Yanzu kuma, lokaci ne da Nijeriya ita ma za ta sa su yi alfahari da ita.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Matan Yobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Next Post

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Related

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano
Bakon Marubuci

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

7 hours ago
Me Ake Nufi Da Ado? 
Bakon Marubuci

Me Ake Nufi Da Ado? 

1 week ago
Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Bakon Marubuci

Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

1 month ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

1 month ago
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata
Bakon Marubuci

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

2 months ago
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari
Bakon Marubuci

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

3 months ago
Next Post
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Takwaransa Na Singapore Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 35 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

Xi Da Takwaransa Na Singapore Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 35 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

October 3, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Yadda Na Ji Bayan Faduwa Zaben 2015 – Jonathan 

Ko Jonathan Zai Iya Ja Da Tinubu A 2027?

October 3, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

October 3, 2025
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

October 3, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

October 3, 2025
NDLEA Ta Kama Kilo 588 Na Miyagun Ƙwayoyi, Ta Ƙona Hekta 6 Na Gonakin Wiwi A Adamawa

NDLEA Ta Kama Kilo 588 Na Miyagun Ƙwayoyi, Ta Ƙona Hekta 6 Na Gonakin Wiwi A Adamawa

October 3, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi

October 3, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

‘Yan Nijeriya Na Karbar Sakamakonsu Da Hannun Hagu A Wajen Tinubu – Atiku

October 3, 2025
Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.