• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Tabbatar Da Tsaro Da Yaki Da Ta’addanci Ya Zama Keta Hakkin Dan Adam?

by CGTN Hausa
1 year ago
Adam

An yi tattaunawa kan batun kare hakkin bil adama tsakanin kasar Sin da Tarayyar Turai (EU) jiya Litinin a birnin Beijing, inda mashawarcin ministan harkokin wajen Sin Miao Deyu, ya bayyana matsayin kasar Sin da ra’ayinta kan batun kare hakkin bil adama.

Yayin tattaunawarsa da mataimakiyar babban direktan hedkwatar sashen Asiya da Pacific ta hukumar gudanarwar EU Paola Pampaloni, ya kuma bayyana ci gaban da Sin ta samu game da batun, tare da nanata niyyar Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin wajen bautawa al’umma.

  • Jirgin Kasa Mai Saurin Tafiya Da Ya Hada Babban Yankin Sin Da Hong kong Ya Fara Aiki
  • Ya Kamata Amurka Ta Cire Cuba Daga Jerin “Kasashe Masu Goyon Bayan Ta’addanci”

Kare hakkin bil adama a ganina shi ne, kasancewar al’umma cikin yanayi na walwala da wadata da tsaro da ci gaba ta kowacce fuska. A duniyar yanzu, da an ambaci kasar Sin, abun da za a tuna shi ne, ci gaban da kasar ta samu ta fuskoki da dama, kuma wannan ba ci gaba ne na fatar baki ba, abu ne da ake gani a aikace, kuma a zahiri, wadanda al’ummar kasar ke mora. Duk wani abu da gwamnatin Sin za ta yi, to abu na farko da ta kan yi la’akari da shi, shi ne moriya da bukatu da muradun jama’arta.

Na kan yi mamaki idan aka ce wai kasar Sin na keta hakkokin bil adama. Shin yaushe tabbatar da tsaron al’umma ya zama keta hakkin bil adama? Yaushe yaki da ta’addanci ya zama keta hakkin bil adama? Yaushe kuma kokarin tabbatar da dunkulewar yankunan kasa ya zama take hakkin bil adama? Idan muka yi nazari, za mu iya fahimta cewa, dukkan abubuwan da ake fakewa da su wajen shafawa kasar bakin fenti, abubuwa ne da za su iya haifar da rikici ko koma baya ga kasar, idan har ba ta dauki matakai masu kwari kamar yadda take yi ba.

Har kullum na kan jinjinawa irin matakan da Sin ke dauka na tabbatar da tsaro da kare moriyarta da ta jama’arta, kasancewar na ga illar ayyukan ta’addanci a zahiri. A ganina da dukkan kasashe za su yi koyi da irin dabarun kasar Sin na jajircewa, to, da duniya ba ta shiga cikin yanayin da take ciki ba.

LABARAI MASU NASABA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Tabbas Sin ta samu ci gaba a bangaren kare hakkin bil adama, domin al’ummarta na cikin kwanciyar hankali da wadata da more rayuwa mai dadi. Ya zama wajibi kasancen yamma su gane cewa, dabaru ko matakansu, ba su ne kadai mafita ba. Haka kuma, ya dace su sakarwa Sin mara ta ci gaba da zabarwa kanta hanyar da ta dace na tafiyar da harkokinta na cikin gida ba tare da sun yi katsalandan ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka
Daga Birnin Sin

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Next Post
Sin Ta Bayyana Matsayi Da Ra’Ayinta a Shawarwari Kan Hakkin Bil Adam Tsakaninta Da Turai

Sin Ta Bayyana Matsayi Da Ra’Ayinta a Shawarwari Kan Hakkin Bil Adam Tsakaninta Da Turai

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.