ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Tabbatar Da Tsaro Da Yaki Da Ta’addanci Ya Zama Keta Hakkin Dan Adam?

by CGTN Hausa
2 years ago
Adam

An yi tattaunawa kan batun kare hakkin bil adama tsakanin kasar Sin da Tarayyar Turai (EU) jiya Litinin a birnin Beijing, inda mashawarcin ministan harkokin wajen Sin Miao Deyu, ya bayyana matsayin kasar Sin da ra’ayinta kan batun kare hakkin bil adama.

Yayin tattaunawarsa da mataimakiyar babban direktan hedkwatar sashen Asiya da Pacific ta hukumar gudanarwar EU Paola Pampaloni, ya kuma bayyana ci gaban da Sin ta samu game da batun, tare da nanata niyyar Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin wajen bautawa al’umma.

  • Jirgin Kasa Mai Saurin Tafiya Da Ya Hada Babban Yankin Sin Da Hong kong Ya Fara Aiki
  • Ya Kamata Amurka Ta Cire Cuba Daga Jerin “Kasashe Masu Goyon Bayan Ta’addanci”

Kare hakkin bil adama a ganina shi ne, kasancewar al’umma cikin yanayi na walwala da wadata da tsaro da ci gaba ta kowacce fuska. A duniyar yanzu, da an ambaci kasar Sin, abun da za a tuna shi ne, ci gaban da kasar ta samu ta fuskoki da dama, kuma wannan ba ci gaba ne na fatar baki ba, abu ne da ake gani a aikace, kuma a zahiri, wadanda al’ummar kasar ke mora. Duk wani abu da gwamnatin Sin za ta yi, to abu na farko da ta kan yi la’akari da shi, shi ne moriya da bukatu da muradun jama’arta.

ADVERTISEMENT

Na kan yi mamaki idan aka ce wai kasar Sin na keta hakkokin bil adama. Shin yaushe tabbatar da tsaron al’umma ya zama keta hakkin bil adama? Yaushe yaki da ta’addanci ya zama keta hakkin bil adama? Yaushe kuma kokarin tabbatar da dunkulewar yankunan kasa ya zama take hakkin bil adama? Idan muka yi nazari, za mu iya fahimta cewa, dukkan abubuwan da ake fakewa da su wajen shafawa kasar bakin fenti, abubuwa ne da za su iya haifar da rikici ko koma baya ga kasar, idan har ba ta dauki matakai masu kwari kamar yadda take yi ba.

Har kullum na kan jinjinawa irin matakan da Sin ke dauka na tabbatar da tsaro da kare moriyarta da ta jama’arta, kasancewar na ga illar ayyukan ta’addanci a zahiri. A ganina da dukkan kasashe za su yi koyi da irin dabarun kasar Sin na jajircewa, to, da duniya ba ta shiga cikin yanayin da take ciki ba.

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Tabbas Sin ta samu ci gaba a bangaren kare hakkin bil adama, domin al’ummarta na cikin kwanciyar hankali da wadata da more rayuwa mai dadi. Ya zama wajibi kasancen yamma su gane cewa, dabaru ko matakansu, ba su ne kadai mafita ba. Haka kuma, ya dace su sakarwa Sin mara ta ci gaba da zabarwa kanta hanyar da ta dace na tafiyar da harkokinta na cikin gida ba tare da sun yi katsalandan ba.

Adam
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Daga Birnin Sin

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Next Post
Sin Ta Bayyana Matsayi Da Ra’Ayinta a Shawarwari Kan Hakkin Bil Adam Tsakaninta Da Turai

Sin Ta Bayyana Matsayi Da Ra’Ayinta a Shawarwari Kan Hakkin Bil Adam Tsakaninta Da Turai

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.