• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Za A Kawo Karshen Karancin Man Fetur?

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Yaushe Za A Kawo Karshen Karancin Man Fetur?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Har sai  yaushe ne za a kawo karshen wannan karancin man? tambayar da ke bakin kusan dukkan ‘yan Nijeriya ke nan a ‘yan kwanakin nan. Nijeriya na fuskantar matsanancin karaci da tsadar man fetur, abin da ke tsayar da harkokin zirga-zirga da kasuwanci cik a wasu sassan kasa, ya kuma haifar da tsadar kayayyakin masarufi da al’murran yau da kullum, wannan kuma ya sa al’umma tunanin gaskiyar ko janye tallafin man fetur da aka cewar zai kai ga magance matsalolin da ake fuskanta tattare da albarkatun man fetur a Nijeriya za a kai ga ganin karshensu ko dai abin ya zama labari ke nan kawai?.

A ranar 29 ga watan Mayu 2023 da Shugaban kasa Tinubu ya sanar da janye tallafin man fetur, abin da ya haifar da karin kudin litar fetur nan take.Al’umma sun dauka wannan tashin gwauron zabon shi ne zai kawo mana karshen karancin man fetur din a Nijeriya.

  • Majalisar Wakilai Ta Umarci CBN Ya Dakatar Da Harajin Tsaron Yanar Gizo
  • Mun Kawo Jam’iyyar AAC Ne Domin Al’ummar Adamawa – Doubli

Amma sai gashi abin bai kasance haka ba.A makon jiya sai gashi dogayen layukan mai a gidajen man fetur sun bayyana a Abuja da wasu jihohin kasar nan,wanda hakan yake tuna mana halin da aka shiga shekarun baya da aka fuskanci irin wannan matsanancin karancin man fetur a Nijeriya.

Kamfanin kula da albarkatun mai na kasa  (NNPCL) ya dora alhakin karancin man a kan kamfanonin masu jigilar man fetur daga wuraren ajiyar mai  da ke  sassan daban daban  na kasar.

Duk da sun bayyana cewa, sun yi maganin matsalar amma a zahiri matsalar na nan har yanzu babu wasu alamun kawo karshen lamarin.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Babu man fetur a gidajen sayar da fetur, kudaden mota sun yi tashin gwauron zabo, takalawa na ci gaba da dandana radadin hauhawar farashin kayan masarufi.

Al’umma ba su gamsu da hujjojin da gwamnati ke bayarwa ba, wadanda suka hada da matsalar zirga-zirga ta masu dakon fetur, fashewar bututun mai, masu satar danyen mai da kuma wai mastalolin da ke fuskanta na karancin kudaden kasashen waje.Wadannan ba sabbin matsaloli ba ne,amma gwamnatotocin da suka gabata da na yanzu duk sun kasa magancewa tare da samar da tabbataciyar hanyar ganin an kawo karshen kwarancin man a fadin tarayyar kasar nan.

A ra’ayinmu, wannan wani abin kunya ne ga kasa,a ce babbar kasa a Afirka kamar Nijeriya da ke a kan gaba a cikin kasashe masu albarkatun man fetur a duniya amma ta kasa samarwa al’ummarta da masana’antunta man da suke bukata ba.Matatun mai 4 da ke Nijeriya sun kasa wadatar da al’umma man da ake bukata, duk kuwa da dimbin kudaden da ake zubawa a duk shekara don gyaransu.

An kasa cika dukkan alkawuran farfado da wadannan manyan kaddarorin kasa. Yayin da matatar mai ta Dangote ke dan ba mu fata, amma hakan ba zai dauke wa gwamnati hakkinta ba na tabbatar da ganin matatun mai na kasa sun dawo suna aiki kamar yadda ya kamata ba, domin al’umma su amfana.

Hasashen da gwamnati ta yi na cewa, matatar mai ta Kaduna zata dawo aiki a karshen shekarar 2024 da kuma cewa, matatar mai ta Fatakwal za ta fara aiki a cikin watan Afrilu na 2024, abu ne da ba za a aminta da shi ba har sai mun gani a kasa.

Hujjar da NNPCL ke bayarwa ta cewa, mastalar dakon mai daga wurin ajiyar  mai da ke Legas ta haifar da karancin man, wata alama ce da ke nuna yadda aka dogara da wurin ajiyar mai guda daya wanda ke Legas wannan kuma ai rashin dabara ne.

In har ana son a kawo karshen wannan karancin man, dole ne a farfado da ayyukan wuraren ajiyar mai 21 da ake da su a fadin tarayyar kasa nan,a kuma yi maganin ‘yan ta’adda masu farfasa bututun mai da ke kai man fetur wuraren ajiyar.

Karin abin takaici a nan kuma shi ne akwai yiwuwar wannan karancin man da mu ke fuskanta ya kazance in har kungiyar masu dakon man fetur suka aiwatar da barazanar da suke yi ta shiga yajin aiki saboda rashin biyansu bashin Naira Biliyan 200 da suke bin gwamnati.

Matsalar karancin man fetur ta ta’azara ne sakamakon rashin tsayayyen tsarin gwamnati a kan tafiyar da harkokin man fetur a Nijeriya da kuma yadda ake tara bashin kamfanonin dakon mai ba tare da an biya su ba, uwa uba kuma shi ne karyewar darajar naira da yadda dala ke kara hauhawa.

Duk da cewa, kamfanin mai na NNPCL ya ce yana da ajiyar man fetur fiye da lita biliyan 1.5, tabbas wannaN ba zai yi maganin matsalar da ake ciki ba, tun da ba a yi maganin matsalar ba tun daga tushenta.

Nijeriya na asarar tiriliyoyin naira sakamakon sace danyen mai da kuma yadda ‘yan ta’adda ke fasa bututun mai amma kuma an kasa kamawa tare da hukunta masu aikata wannan danyen aikin.

A yayin da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da dandana radadin karacin man fetur, al’umma na tunani tare da tambayar wai yaushe ne za a kawo karshen wannan karancin man da ake fuskanta?

Gwamnatocin da suka gabata sun yi nasu kokarin na ganin an kawo karshen matsalar da ke tattrare da karancin man fetur amma har yanzu an kasa gano bakin zare. Gwamnatin Bola Ahmed Tijubu ta gaji wannan matsalar ne amma dole ta samar da hanyar kawo karshena, musamman ganin yadda lamarin ya jefa al’ummar Nijeriya cikin halin ni ‘yasu.

Matsalar karancin man fetur ba abin da ya shafi tattalin arziki kadai ba ne amma ya kuma shafi matsalar tsaron da ake fama da si a sassan Nijeriya.Kasar da ba za ta iya samarwa masa’anantunta, bangaren sufuri man fetur na gudanar da ayyukanta ba tabbas ta shiga halin takura wanda zai haifar mata da koma baya a dukkan harkokin ci gabanta, al’ummarta  kuma za su ci gaba da dauwama a cikin kangin talauci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FeturgwamnatiKarancin MaiNNPCLWahala
ShareTweetSendShare
Previous Post

Peng Liyuan Da Mai Dakin Firaministan Kasar Hungary Sun Ziyarci Makarantar Koyar Da Harsunan Sinanci Da Hungary

Next Post

Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

4 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

10 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

15 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

19 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

20 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Next Post
Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli

Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.