• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Za A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza?

by Lubabatu Lei
2 years ago
Gaza

Kwanan baya, Amurka ta sake jefa kuri’ar nuna rashin amincewa da wani daftarin kudurin da kasar Aljeriya ta gabatar dangane da batun Gaza a kwamitin sulhu na MDD, karo na hudu ke nan da ta jefa kuri’ar rashin amincewa da daftarin kuduri game da batun tsagaita bude wuta a Gaza, tun bayan barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila a watan Oktoban bara.

Hakan ya sa kasashe da dama ciki har da kasar Sin fusata, inda suke ganin cewa, “matakin ya nuna amincewa da kisan kiyashi da ake yi” “Kwamitin sulhu ya shaida wani mummunan babi na daban da Amurka ta rubuta”.

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Dukkan Bangarori Domin Gina Budadden Tsarin Tattalin Arziki Na Duniya

Tun bayan barkewar rikicin, Palasdinawa kusan dubu 30 sun halaka a matakan soja da Isra’ila ta dauka a zirin Gaza, baya ga wasu sama da dubu 70 da suka ji raunuka. Amma me ya sa Amurka ta yi shiru a kan batun tsagaita bude wuta, har ma ta yi kokarin kawo cikas ga kokarin da sauran kasashe suka yi?

A hakika, huldar dake tsakaninta da Isra’ila na da muhimmiyar ma’ana gare ta. Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya taba bayyanawa a jawabin da ya gabatar a shekarun da suka gabata cewa, “Da a ce babu Isra’ila, to Amurka za ta kirkiro Isra’ila don kare muradunta a yankin gabas ta tsakiya.” Kasancewar Isra’ila kasa ce mai karfi ta fannin soja da leken asiri, Amurka na daukarta a matsayin babban makaminta a yankin gabas ta tsakiya, abin da ya sa Amurka ta dade tana nuna goyon baya ga Isra’ila. A sa’i daya kuma, daidai kamar yadda ta yi a yakin Afghanistan da rikici a tsakanin Rasha da Ukraine, masana’antun samar da makaman soja na Amurka da sauran masu ruwa da tsaki sun ci kazamar riba sakamakon rikicin da ya barke.

Amurka tana cin gajiya idan ta nuna goyon baya ga Isra’ila, kuma a gaban tarin riba, abin da a bakinta na wai “dimokuradiyya da hakkin dan Adam” ba kome ba ne.
Yanzu haka sabon zagayen shawarwari kan batun tsagaita bude wuta a zirin Gaza na gudana a kasar Qatar. Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya bayyana a jiya 26 ga wata cewa, an kusan cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta a tsakanin Isra’ila da Hamas, kuma ya yi fatan ganin sassan biyu za su cimma tsagaita bude wuta kafin Litinin mai zuwa.

LABARAI MASU NASABA

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Da fatan shugaba Biden ya fadi gaskiya, da fatan kuma da gaske ne Amurka na sulhuntawa yadda ya kamata a wannan karo. Muna fatan ganin an tabbatar wa al’ummar zirin Gaza da zaman lafiya a dab da zuwan watan Ramadan mai tsarki. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?
Ra'ayi Riga

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
Ra'ayi Riga

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Saliyo

Shugaba Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Saliyo

LABARAI MASU NASABA

Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025

Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

October 25, 2025
Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

October 25, 2025
An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC

An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.