• English
  • Business News
Monday, July 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Za A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza?

by Lubabatu Lei
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Yaushe Za A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan baya, Amurka ta sake jefa kuri’ar nuna rashin amincewa da wani daftarin kudurin da kasar Aljeriya ta gabatar dangane da batun Gaza a kwamitin sulhu na MDD, karo na hudu ke nan da ta jefa kuri’ar rashin amincewa da daftarin kuduri game da batun tsagaita bude wuta a Gaza, tun bayan barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila a watan Oktoban bara.

Hakan ya sa kasashe da dama ciki har da kasar Sin fusata, inda suke ganin cewa, “matakin ya nuna amincewa da kisan kiyashi da ake yi” “Kwamitin sulhu ya shaida wani mummunan babi na daban da Amurka ta rubuta”.

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Dukkan Bangarori Domin Gina Budadden Tsarin Tattalin Arziki Na Duniya

Tun bayan barkewar rikicin, Palasdinawa kusan dubu 30 sun halaka a matakan soja da Isra’ila ta dauka a zirin Gaza, baya ga wasu sama da dubu 70 da suka ji raunuka. Amma me ya sa Amurka ta yi shiru a kan batun tsagaita bude wuta, har ma ta yi kokarin kawo cikas ga kokarin da sauran kasashe suka yi?

A hakika, huldar dake tsakaninta da Isra’ila na da muhimmiyar ma’ana gare ta. Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya taba bayyanawa a jawabin da ya gabatar a shekarun da suka gabata cewa, “Da a ce babu Isra’ila, to Amurka za ta kirkiro Isra’ila don kare muradunta a yankin gabas ta tsakiya.” Kasancewar Isra’ila kasa ce mai karfi ta fannin soja da leken asiri, Amurka na daukarta a matsayin babban makaminta a yankin gabas ta tsakiya, abin da ya sa Amurka ta dade tana nuna goyon baya ga Isra’ila. A sa’i daya kuma, daidai kamar yadda ta yi a yakin Afghanistan da rikici a tsakanin Rasha da Ukraine, masana’antun samar da makaman soja na Amurka da sauran masu ruwa da tsaki sun ci kazamar riba sakamakon rikicin da ya barke.

Amurka tana cin gajiya idan ta nuna goyon baya ga Isra’ila, kuma a gaban tarin riba, abin da a bakinta na wai “dimokuradiyya da hakkin dan Adam” ba kome ba ne.
Yanzu haka sabon zagayen shawarwari kan batun tsagaita bude wuta a zirin Gaza na gudana a kasar Qatar. Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya bayyana a jiya 26 ga wata cewa, an kusan cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta a tsakanin Isra’ila da Hamas, kuma ya yi fatan ganin sassan biyu za su cimma tsagaita bude wuta kafin Litinin mai zuwa.

Labarai Masu Nasaba

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

Da fatan shugaba Biden ya fadi gaskiya, da fatan kuma da gaske ne Amurka na sulhuntawa yadda ya kamata a wannan karo. Muna fatan ganin an tabbatar wa al’ummar zirin Gaza da zaman lafiya a dab da zuwan watan Ramadan mai tsarki. (Mai Zane: Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGazaIsra'ilaYaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Tsinci Kansa A Gidan Yari Bayan Kin Biyan Kuɗin Bokiti 5 Na Giya Da Ya Sha A Yola

Next Post

Shugaba Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Saliyo

Related

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?
Ra'ayi Riga

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

2 days ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

3 days ago
Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”
Ra'ayi Riga

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

4 days ago
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

6 days ago
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

1 week ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

2 weeks ago
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Saliyo

Shugaba Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Saliyo

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

July 21, 2025
Ƴan Bindiga Sun Tafka Gagarumar Sata A Bauchi, Sun Tafi Da Mutane 4

Ƴan Bindiga Sun Tafka Gagarumar Sata A Bauchi, Sun Tafi Da Mutane 4

July 21, 2025
Yadda Gwamnan Katsina Ya Tsira Daga Hatsarin Mota

Yadda Gwamnan Katsina Ya Tsira Daga Hatsarin Mota

July 21, 2025
Saurayi Ya Kashe Budurwarsa, Yace Sharrin Ƙwaya Ne

Saurayi Ya Kashe Budurwarsa, Yace Sharrin Ƙwaya Ne

July 21, 2025
Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

July 20, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

‘Ka Da Ki Kuskura Ki Zo Majalisar Tarayya’, Majalisar Dattawa Ta Sake Yi Wa Natasha Gargaɗi

July 20, 2025
An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

July 20, 2025
Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

July 20, 2025
Jimillar Sayar Da Kayayyakin Masarufi Ta Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Triliyan 50 A Bana

Jimillar Sayar Da Kayayyakin Masarufi Ta Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Triliyan 50 A Bana

July 20, 2025
Mataimakin Shugaban Kamfanin Panasonic: Kamfanonin Sin Dake Samar Da Sassan Kayayyaki Ga Kamfaninsa Sun Kai Dubu 6

Mataimakin Shugaban Kamfanin Panasonic: Kamfanonin Sin Dake Samar Da Sassan Kayayyaki Ga Kamfaninsa Sun Kai Dubu 6

July 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.