ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Za A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza?

by Lubabatu Lei
2 years ago
Gaza

Kwanan baya, Amurka ta sake jefa kuri’ar nuna rashin amincewa da wani daftarin kudurin da kasar Aljeriya ta gabatar dangane da batun Gaza a kwamitin sulhu na MDD, karo na hudu ke nan da ta jefa kuri’ar rashin amincewa da daftarin kuduri game da batun tsagaita bude wuta a Gaza, tun bayan barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila a watan Oktoban bara.

Hakan ya sa kasashe da dama ciki har da kasar Sin fusata, inda suke ganin cewa, “matakin ya nuna amincewa da kisan kiyashi da ake yi” “Kwamitin sulhu ya shaida wani mummunan babi na daban da Amurka ta rubuta”.

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Dukkan Bangarori Domin Gina Budadden Tsarin Tattalin Arziki Na Duniya

Tun bayan barkewar rikicin, Palasdinawa kusan dubu 30 sun halaka a matakan soja da Isra’ila ta dauka a zirin Gaza, baya ga wasu sama da dubu 70 da suka ji raunuka. Amma me ya sa Amurka ta yi shiru a kan batun tsagaita bude wuta, har ma ta yi kokarin kawo cikas ga kokarin da sauran kasashe suka yi?

ADVERTISEMENT

A hakika, huldar dake tsakaninta da Isra’ila na da muhimmiyar ma’ana gare ta. Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya taba bayyanawa a jawabin da ya gabatar a shekarun da suka gabata cewa, “Da a ce babu Isra’ila, to Amurka za ta kirkiro Isra’ila don kare muradunta a yankin gabas ta tsakiya.” Kasancewar Isra’ila kasa ce mai karfi ta fannin soja da leken asiri, Amurka na daukarta a matsayin babban makaminta a yankin gabas ta tsakiya, abin da ya sa Amurka ta dade tana nuna goyon baya ga Isra’ila. A sa’i daya kuma, daidai kamar yadda ta yi a yakin Afghanistan da rikici a tsakanin Rasha da Ukraine, masana’antun samar da makaman soja na Amurka da sauran masu ruwa da tsaki sun ci kazamar riba sakamakon rikicin da ya barke.

Amurka tana cin gajiya idan ta nuna goyon baya ga Isra’ila, kuma a gaban tarin riba, abin da a bakinta na wai “dimokuradiyya da hakkin dan Adam” ba kome ba ne.
Yanzu haka sabon zagayen shawarwari kan batun tsagaita bude wuta a zirin Gaza na gudana a kasar Qatar. Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya bayyana a jiya 26 ga wata cewa, an kusan cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta a tsakanin Isra’ila da Hamas, kuma ya yi fatan ganin sassan biyu za su cimma tsagaita bude wuta kafin Litinin mai zuwa.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Da fatan shugaba Biden ya fadi gaskiya, da fatan kuma da gaske ne Amurka na sulhuntawa yadda ya kamata a wannan karo. Muna fatan ganin an tabbatar wa al’ummar zirin Gaza da zaman lafiya a dab da zuwan watan Ramadan mai tsarki. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

Gaza
Lubabatu Lei
+ postsBio
  • Lubabatu Lei
    https://hausa.leadership.ng/author/lubabatu-lei/
    Duniya Na Fatan Ganin An Tabbatar Da “Faster, Higher, Stronger –Together” A Wasannin Olympics Na Los Angeles
  • Lubabatu Lei
    https://hausa.leadership.ng/author/lubabatu-lei/
    Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Saliyo

Shugaba Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Saliyo

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.