ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Za A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza?

by Lubabatu Lei
2 years ago
Gaza

Kwanan baya, Amurka ta sake jefa kuri’ar nuna rashin amincewa da wani daftarin kudurin da kasar Aljeriya ta gabatar dangane da batun Gaza a kwamitin sulhu na MDD, karo na hudu ke nan da ta jefa kuri’ar rashin amincewa da daftarin kuduri game da batun tsagaita bude wuta a Gaza, tun bayan barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila a watan Oktoban bara.

Hakan ya sa kasashe da dama ciki har da kasar Sin fusata, inda suke ganin cewa, “matakin ya nuna amincewa da kisan kiyashi da ake yi” “Kwamitin sulhu ya shaida wani mummunan babi na daban da Amurka ta rubuta”.

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Dukkan Bangarori Domin Gina Budadden Tsarin Tattalin Arziki Na Duniya

Tun bayan barkewar rikicin, Palasdinawa kusan dubu 30 sun halaka a matakan soja da Isra’ila ta dauka a zirin Gaza, baya ga wasu sama da dubu 70 da suka ji raunuka. Amma me ya sa Amurka ta yi shiru a kan batun tsagaita bude wuta, har ma ta yi kokarin kawo cikas ga kokarin da sauran kasashe suka yi?

ADVERTISEMENT

A hakika, huldar dake tsakaninta da Isra’ila na da muhimmiyar ma’ana gare ta. Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya taba bayyanawa a jawabin da ya gabatar a shekarun da suka gabata cewa, “Da a ce babu Isra’ila, to Amurka za ta kirkiro Isra’ila don kare muradunta a yankin gabas ta tsakiya.” Kasancewar Isra’ila kasa ce mai karfi ta fannin soja da leken asiri, Amurka na daukarta a matsayin babban makaminta a yankin gabas ta tsakiya, abin da ya sa Amurka ta dade tana nuna goyon baya ga Isra’ila. A sa’i daya kuma, daidai kamar yadda ta yi a yakin Afghanistan da rikici a tsakanin Rasha da Ukraine, masana’antun samar da makaman soja na Amurka da sauran masu ruwa da tsaki sun ci kazamar riba sakamakon rikicin da ya barke.

Amurka tana cin gajiya idan ta nuna goyon baya ga Isra’ila, kuma a gaban tarin riba, abin da a bakinta na wai “dimokuradiyya da hakkin dan Adam” ba kome ba ne.
Yanzu haka sabon zagayen shawarwari kan batun tsagaita bude wuta a zirin Gaza na gudana a kasar Qatar. Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya bayyana a jiya 26 ga wata cewa, an kusan cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta a tsakanin Isra’ila da Hamas, kuma ya yi fatan ganin sassan biyu za su cimma tsagaita bude wuta kafin Litinin mai zuwa.

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Da fatan shugaba Biden ya fadi gaskiya, da fatan kuma da gaske ne Amurka na sulhuntawa yadda ya kamata a wannan karo. Muna fatan ganin an tabbatar wa al’ummar zirin Gaza da zaman lafiya a dab da zuwan watan Ramadan mai tsarki. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

Gaza
Lubabatu Lei
+ postsBio
  • Lubabatu Lei
    https://hausa.leadership.ng/author/lubabatu-lei/
    Duniya Na Fatan Ganin An Tabbatar Da “Faster, Higher, Stronger –Together” A Wasannin Olympics Na Los Angeles
  • Lubabatu Lei
    https://hausa.leadership.ng/author/lubabatu-lei/
    Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

MASU ALAKA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Saliyo

Shugaba Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Saliyo

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.