• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaya Za A Cimma “Tsaro tare”? Dandalin Xiangshan Ya Gabatar Da Wasu Tunani

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yaya Za A Cimma “Tsaro tare”? Dandalin Xiangshan Ya Gabatar Da Wasu Tunani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An rufe taron dandalin tattaunawa kan batun tsaro na Xiangshan karo na 10 a birnin Beijing jiya Talata. Yayin taron, wakilai fiye da 1800 daga kasashe da yankuna da kuma kungiyoyin kasa da kasa sama da 100 sun gudanar da tattaunawa tare da musayar ra’ayoyi bisa taken “Tsaro na bai daya, zaman lafiya mai dorewa”, adadin mahalarta taron da mukamansu duka sun kai wani matsayin da ba a taba gani a da ba.

Yaya za a cimma buri na “tabbatar da tsaro tare”? Ta hanyar tattaunawar da aka yi a dandalin Xiangshan na Beijing, an samu kyakkyawar fahimta.

  • Hausawa ‘Yan Kasuwar Shanu Na Neman Sasantawa Da Gwamnatin Abiya
  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Tauraron Dan Adam Na Tianhui-5 

Ko shakka babu, manyan kasashe suna da nauyi da muhimmanci na musamman wajen wanzar da zaman lafiya da tsaron kasa da kasa. A yayin taron, Xanthi Carras, direktar sashen kula da harkokin kasar Sin a ofishin mai ba da taimako ga mataimakin sakataren ma’aikatar tsaron kasar Amurka ta halarci taron a madadin ma’aikatar tsaron kasar Amurka.

Ana sa ran cewa, bangarorin Amurka da Sin za su iya kai zuciya nesa su yi kokarin samar da wani kyakkyawan yanayi, ta yadda za a iya tabbatar da ganin dangantakar dake tsakanin rundunonin soja na kasashen biyu ta samu ci gaba cikin kwanciyar hankali kamar yadda ake fata.

Idan ana son cimma buri na “tabbatar da tsaro tare”, abu mai muhimmanci shi ne tsayawa tsayin daka kan warware sabani da rikici dake kasancewa tsakanin kasa da kasa ta hanyar tattaunawa da tuntubar juna cikin lumana. A wannan dandalin, an gayyaci wakilan wasu bangarorin da suke yin rikici da juna, kamar wakilan Isra’ila da na kasashen Larabawa, da Rasha da Ukraine don yin tattaunawa da tuntubar juna fuska da fuska.

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

Har yanzu, wasu manyan kasashen yamma suna bin ra’ayinsu na tabbatar da “cikakken tsaron kansu”, har ma suna bin tunanin yakin cacar baki, da kuma haddasa fito na fito tsakanin bangarori daban daban, da kuma haifar da kalubale mai sarkakiya ga yanayin kasa da kasa. Masana mahalarta taron suna ganin cewa, dandalin Xiangshan ya ba dukkan kasashen yammacin duniya damar sani da kuma fahimtar matsayi da ra’ayoyi daban daban na sauran kasashen duniya. Hakan yana da matukar muhimmanci ga kasashen duniya da su yi kokarin yin hadin gwiwa domin samun nasara tare. (Safiyah Ma)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJapanSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kyawawan Manufofin Tattalin Arzikin Sin Na Kara Karfafawa Kamfanonin Ketare Gwiwar Shiga Babbar Kasuwar Kasar

Next Post

Dankwambo Ya Ce Daga Yanzu Gwamnatin Gombe Ta Daina Biyansa Fansho Ya Yafe

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

16 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

18 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

19 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

20 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

2 days ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

2 days ago
Next Post
Dankwambo Ya Ce Daga Yanzu Gwamnatin Gombe Ta Daina Biyansa Fansho Ya Yafe

Dankwambo Ya Ce Daga Yanzu Gwamnatin Gombe Ta Daina Biyansa Fansho Ya Yafe

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.