• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yobe Ta Arewa: Machina Ya Sake Samun Nasara Yayin Da Kotu Ta Kori Karar Da Aka Sake Shigarwa A Kansa 

by Sadiq
3 years ago
Machina

Tsohon dan takarar kujerar Sanatan Yobe ta Arewa a Jihar Yobe, Abubakar Abubakar Jinjiri, ya janye karar da ya shigar a kan dan takarar kujerar sanata na jam’iyyar APC, Bashir Sheriff Machina da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da kuma jam’iyyar APC. 

Sanata Jinjiri, ta bakin lauyansa, Barista Usman Lukman Nuhu, ya shaida wa mai shari’a Fadima Aminu ta babbar kotun tarayya da ke zamanta a Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, cewa an shigar da sanarwar dakatar da wadanda ake kara a kan lamarin.

  • Gobara Ta Tashi A Wani Gidan Man Sayar Da Gas A Fatakwal 
  • Karancin Man Fetur: NSCDC Ta Gargadi Gidajen Mai Kan Boye Man Fetur

LEADERSHIP ta tattaro cewa lamarin ya faru ne jim kadan bayan da aka bukaci a saurari karar a ranar Laraba.

Barista Nuhu ya sanar da cewar Jinjiri da ya janye karar sannan ya roki kotu da ta dakatar da shari’ar tare da bayar da umarnin soke karar.

Lauyan Machina, Barista Mohammed Ngumurumi wanda ya rike da takaitaccen bayanin Ibrahim Bawa, SAN, ya roki kotun da ta yi watsi da karar maimakon ta soke ta.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Sauran wadanda ake tuhuma kuma ba su yi adawa da sanarwar janye mai karar ba.

A hukuncin da ta yanke, mai shari’a Fadima Aminu ta bayyana cewa Jinjiri na da damar shigar da sanarwar janyewar kararsa.

Ta ce sanarwar dakatarwar ta na nan daram saboda haka ta yi watsi da karar kamar yadda lauyan Machina ya bukata.

A ranar 17 ga watan Yuni ne Jinjiri ya garzaya babbar kotun tarayya da ke Damaturu tare da gabatar da karar gabanin zabe yana kalubalantar takarar Bashir Machina wanda ya lashe zaben fidda gwanin dan takarar Sanata na jam’iyyar APC na mazabar Yobe ta Arewa a ranar 2 ga watan Mayu.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a makonnin da suka gabata ne kotun ta ayyana Machina a matsayin wanda ya cancanta a matsayin zababben dan takarar kujerar Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC a zaben 2023, wanda hakan ya kawo karshen cece-kuce da suka dabaibaye jam’iyyar APC a Yobe ta Arewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.