• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yobe Ta Arewa: Machina Ya Sake Samun Nasara Yayin Da Kotu Ta Kori Karar Da Aka Sake Shigarwa A Kansa 

by Sadiq
3 years ago
Machina

Tsohon dan takarar kujerar Sanatan Yobe ta Arewa a Jihar Yobe, Abubakar Abubakar Jinjiri, ya janye karar da ya shigar a kan dan takarar kujerar sanata na jam’iyyar APC, Bashir Sheriff Machina da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da kuma jam’iyyar APC. 

Sanata Jinjiri, ta bakin lauyansa, Barista Usman Lukman Nuhu, ya shaida wa mai shari’a Fadima Aminu ta babbar kotun tarayya da ke zamanta a Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, cewa an shigar da sanarwar dakatar da wadanda ake kara a kan lamarin.

  • Gobara Ta Tashi A Wani Gidan Man Sayar Da Gas A Fatakwal 
  • Karancin Man Fetur: NSCDC Ta Gargadi Gidajen Mai Kan Boye Man Fetur

LEADERSHIP ta tattaro cewa lamarin ya faru ne jim kadan bayan da aka bukaci a saurari karar a ranar Laraba.

Barista Nuhu ya sanar da cewar Jinjiri da ya janye karar sannan ya roki kotu da ta dakatar da shari’ar tare da bayar da umarnin soke karar.

Lauyan Machina, Barista Mohammed Ngumurumi wanda ya rike da takaitaccen bayanin Ibrahim Bawa, SAN, ya roki kotun da ta yi watsi da karar maimakon ta soke ta.

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

Sauran wadanda ake tuhuma kuma ba su yi adawa da sanarwar janye mai karar ba.

A hukuncin da ta yanke, mai shari’a Fadima Aminu ta bayyana cewa Jinjiri na da damar shigar da sanarwar janyewar kararsa.

Ta ce sanarwar dakatarwar ta na nan daram saboda haka ta yi watsi da karar kamar yadda lauyan Machina ya bukata.

A ranar 17 ga watan Yuni ne Jinjiri ya garzaya babbar kotun tarayya da ke Damaturu tare da gabatar da karar gabanin zabe yana kalubalantar takarar Bashir Machina wanda ya lashe zaben fidda gwanin dan takarar Sanata na jam’iyyar APC na mazabar Yobe ta Arewa a ranar 2 ga watan Mayu.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a makonnin da suka gabata ne kotun ta ayyana Machina a matsayin wanda ya cancanta a matsayin zababben dan takarar kujerar Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC a zaben 2023, wanda hakan ya kawo karshen cece-kuce da suka dabaibaye jam’iyyar APC a Yobe ta Arewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus
Manyan Labarai

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

October 19, 2025
Yadda Ake Alkaki

Yadda Ake Alkaki

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.