• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yobe Ta Arewa: Machina Ya Sake Samun Nasara Yayin Da Kotu Ta Kori Karar Da Aka Sake Shigarwa A Kansa 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Yobe Ta Arewa: Machina Ya Sake Samun Nasara Yayin Da Kotu Ta Kori Karar Da Aka Sake Shigarwa A Kansa 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon dan takarar kujerar Sanatan Yobe ta Arewa a Jihar Yobe, Abubakar Abubakar Jinjiri, ya janye karar da ya shigar a kan dan takarar kujerar sanata na jam’iyyar APC, Bashir Sheriff Machina da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da kuma jam’iyyar APC. 

Sanata Jinjiri, ta bakin lauyansa, Barista Usman Lukman Nuhu, ya shaida wa mai shari’a Fadima Aminu ta babbar kotun tarayya da ke zamanta a Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, cewa an shigar da sanarwar dakatar da wadanda ake kara a kan lamarin.

  • Gobara Ta Tashi A Wani Gidan Man Sayar Da Gas A Fatakwal 
  • Karancin Man Fetur: NSCDC Ta Gargadi Gidajen Mai Kan Boye Man Fetur

LEADERSHIP ta tattaro cewa lamarin ya faru ne jim kadan bayan da aka bukaci a saurari karar a ranar Laraba.

Barista Nuhu ya sanar da cewar Jinjiri da ya janye karar sannan ya roki kotu da ta dakatar da shari’ar tare da bayar da umarnin soke karar.

Lauyan Machina, Barista Mohammed Ngumurumi wanda ya rike da takaitaccen bayanin Ibrahim Bawa, SAN, ya roki kotun da ta yi watsi da karar maimakon ta soke ta.

Labarai Masu Nasaba

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Sauran wadanda ake tuhuma kuma ba su yi adawa da sanarwar janye mai karar ba.

A hukuncin da ta yanke, mai shari’a Fadima Aminu ta bayyana cewa Jinjiri na da damar shigar da sanarwar janyewar kararsa.

Ta ce sanarwar dakatarwar ta na nan daram saboda haka ta yi watsi da karar kamar yadda lauyan Machina ya bukata.

A ranar 17 ga watan Yuni ne Jinjiri ya garzaya babbar kotun tarayya da ke Damaturu tare da gabatar da karar gabanin zabe yana kalubalantar takarar Bashir Machina wanda ya lashe zaben fidda gwanin dan takarar Sanata na jam’iyyar APC na mazabar Yobe ta Arewa a ranar 2 ga watan Mayu.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a makonnin da suka gabata ne kotun ta ayyana Machina a matsayin wanda ya cancanta a matsayin zababben dan takarar kujerar Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC a zaben 2023, wanda hakan ya kawo karshen cece-kuce da suka dabaibaye jam’iyyar APC a Yobe ta Arewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCHukunciJinjiriKaraKotuMachinaShari'aYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gobara Ta Tashi A Wani Gidan Man Sayar Da Gas A Fatakwal 

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu

Related

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

1 hour ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

3 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

6 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

7 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

7 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

8 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.