ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yobe Ta Arewa: Yadda Take Kayawa A Yakin Neman Zaben Bashir Machina Bayan Kada Ahmad Lawan

by Muhammad Maitela
4 years ago
Machina

Duk da kiki-kaka da zaman tankiya da ake ci gaba da fuskanta tsakanin magoya bayan Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmad Lawan da bangaren Hon. Bashir Machina, kan takarar Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC, hakan ba ta hana gudanar da gangamin yakin neman zaben ba.

Muhammed Dauda Sa’id (Gaskanta) shi ne Ko’odinatan yakin neman zaben dan takarar Sanatan Yobe ta Arewa, Hon. Bashir Machina, inda ya bayyana wa wakilinmu a jihar Yobe cewa, duk da rashin fahimtar da wasu daga cikin magoya bayan Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmad Lawan suka yi wa al’amarin, amma hakan bai hana yakin neman zaben samun gagarumar tarba daga al’ummar yankin ba.

  • Ban Taba Nadamar Kai Kara Kotu Kan Takarata Ba – Machina

Ya ce, a tarukan da suka gudanar a kananan hukumomin Nguru, Karasuwa, Machina da Gashuwa, ya gudana cikin nasara tare da nuna goyon bayan dubun-dubatar jama’a. Ya ce wannan alamu ne da suka nuna al’ummar yankin suna cike da shaukin samun canjin sabon hannu don ya jagoranci Yobe ta Arewa zuwa ga samun ci gaba mai dorewa, bayan zaben 2023.

ADVERTISEMENT

“Kuma a matsayina na Ko’odinatan yakin neman zaben sa, abin alfahari ne gareni bisa yawan jama’ar da suka fito maza da mata, yara da manya- jama’a ne ke tururuwa daga Ofishin Yan-sanda na bakin garin Gashuwa zuwa kofar Fadar Mai Bade; tazarar kilomita daya da digo biyar, sai da ya kwashe awanni biyu da minti 5 kafin ya isa Kofar Fada.

Saboda yadda jama’a ke daukin samun sabon canji.”
Hon. Gaskanta ya kara da cewa, wannan karbuwa da Hon. Bashir Machina yake samu alamun nasara ne, saboda dukanmu ya’yan jam’iyyar APC ne, kuma mutane ba a shirye suke su bar jam’iyyar ba, masu da’a da biyayya ne ga jam’iyyar APC. “Babu yadda za a yi irin wannan sabanin da aka samu ya hana cikakken dan jam’iyyar yaki zabar mutumin da jam’iyyar ta tsayar ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Sannan wannan rigimar bata yi tsamin irin wadda ta faru tsakanin marigayi Gwamna Mamman B. Ali da marigayi Sanata Usman Al-Bashir ba, saboda shi Sanata Ahmed Lawan bai yi takarar Sanatan Yobe ta Arewa ba, face kawai shugaban jam’iyyar APC na kasa ne yake neman ya kwace kujerar ya bashi.”

Ya kara da cewa, “Sannan kuma shi Shugaban jam’iyyar APC na kasa bai fito ta hanyar lalama ba, saboda mu ‘ya’ya ne, kanne, kuma iyaye a wata fuskar, kuma da ace an bukaci zama da Hon. Bashir Machina da mu magoya bayan sa, a nemi taimakonmu a lokacin da Sanata Ahmed Lawan ya fadi zaben fidda-gwani na Shugaban kasa, a nemi alfarmar a bar masa takarar Sanatan Yobe ta Arewa, wannan daidai ce. Amma ba ta nuna karfin shugabancin jam’iyya ba.” Ya nanata.

“Kuma matakin da Hon. Bashir Machina ya dauka na zuwa kotu daidai ne, saboda ba a nemeshi ta sulhu ba, sai ake neman ayi masa ‘ko da tsaiya-tsiya, ko da karfin tsiya’ ka ga dole ya garzaya inda za a kwata masa hakkinsa; inda mu mabiyansa muka goya masa baya har Allah ya bashi nasara a kotu karon farko da na biyu. Ko in Sha Allah yadda jama’a suka yi maraba dashi haka zasu jefa masa kuri’a cikin nasara.”

Ko’odinatan ya kara da cewa, kwamitin yakin neman zaben Hon. Bashir Machina suna kai-komo wajen lallashin magoya bayan Shugaban Majalisar Dattawan, suna binsu gida-gida tare da basu hakuri, ya ce, “Shima Sanata Ahmed Lawan zamu nada kwamiti mu sameshi har gida mu bashi hakuri.

Saboda dukanmu ya’yan jam’iyyar APC ne kuma a karkashin Limamin Sulhu, Hon. Mai Mala Buni, wanda kowa ya san matsayin sa na sulhunta ya’yan jam’iyyar APC a matakin kasa ba a Yobe kadai ba.”

A hannu guda kuma, Muhammed Dauda Sa’id ya kara da cewa, babban kuskure ne wani ya zargi Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni kan goyon bayan wani bangare ko nuna bambanci tsakani.

Ya ce rashin adalci ne a zargi Gwamna saboda shi uban kowa ne kuma babu wata hujja ko shaida a Kan hakan, face kawai zance ne maras tushe da makama. Ya ce, “Kowa ya san wanda ya haddasa mana wannan fitina ta cikin gida, ba kowa bane face Shugaban jam’iyyar APC na kasa.”

A karshe ya bayyana cewa, “Muna kira ga daukwacin al’ummar wannan yanki da jihar Yobe baki daya, kowa ya hakura a hada kai ayi abu guda kuma mu fuskanci ci gaban yankin mu da jiharmu dama kasa baki daya. Kuma muna kira ga matasanmu don Allah ayi hakuri a mutunta juna kuma a guji bangar siyasa a mutunta juna.

Sannan bama goyon bayan duk wani aiki ko kamalan cin zarafi da bayyana kiyayya ga junanumu, muna ba kowa hakuri azo ayi aiki tare.” Ya nanata.

Machina
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Machina
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Gurbacewar Tarbiyyar Matasa:  Wasika Zuwa Ga Iyaye!

Gurbacewar Tarbiyyar Matasa: Wasika Zuwa Ga Iyaye!

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.