• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin Yin Katsa Landan Ba Zai Dakile Ci Gaban Yankin HK Ba

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
HK
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar dai yadda aka yi tsammani, bayan majalissar dokokin HK ta zartas da kudurin dokar tsaron kasa da gagarumin rinjaye a baya bayan nan, ta kuma cimma nasarar kammala sashe na 23, na dokar gudanarwar yankin na musamman na Sin a ranar 19 ga watan nan, wasu sassa daga kasashen yamma sun zabura, wajen fara sukar wannan mataki, suna masu cewa hanya ce ta dakushe ‘yancin bil adama, kana wasu sun rika nuna shakku, game da yanayin da yankin na HK zai shiga ta fuskar hada hadar kasuwanci.

Amma abun tambaya a nan shi ne, shin wajibi ne a samar da wannan doka ta tsaro? Kuma mene ne ma’anarta ga yankin HK? Alal hakika, zarge-zarge, da kazafi da wadancan sassa suka yiwa Sin ba su da tushe ko makama. Kawai dai akwai wasu mutane a kasashen yamma, dake gudanar da wasan kwaikwayon siyasa da suka saba.

  • Yadda Dimokaradiyya Ke Aiki A Kasar Sin
  • Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2

Ya zuwa yau, mutane sun kara fahimtar wajibcin wannan doka ta tsaron kasa, la’akari da yamutsin da yankin HK ya sha fama da shi mai nasaba da yunkurin “samun ‘yancin kai”, da tashin hankalin da ya biyo bayan hakan, yayin gyaran dokokin jagorancin yankin.

A shekarar 2020 ne aka tsara dokar tsaron kasa ta yankin HK, aka kuma aiwatar da ita, wadda ta zama ginshikin samun wadata da daidaito a yankin. Yanzu haka shekaru 3 sun shude bayan wannan ci gaba, kuma tuni yankin HK ya sauya daga wurin da ya sha fama da tashe tashen hankula, zuwa wuri mai cikakken tsarin jagoranci da walwala. To sai dai kuma a daya hannun, kalubalen tsaron kasa da yankin ke fuskanta har yanzu yana da sarkakiya da tsanani.

Wannan doka ta tsaron kasa ta HK, da sauran dokokin da ake aiwatarwa a yankin na musamman na Sin, ba su kai ga wadatarwa wajen shawo kan dukkanin dabi’u, da ayyuka dake iya haifar da barazana ga tsaron kasa ba. Zartas da wannan doka ta yankin HK a wannan karo, na da nasaba da aiwatar da kudurorin tsaron kasa na HK, da cike gibin manufar tabbatar da tsaro a HK, da tabbatar da wanzuwar daidaito na dogon lokaci a HK, da ma cimma nasarar gudanar da manufar nan ta “kasa daya tsarin mulki biyu” bisa daidaito.  (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Daure Barawon Alkur’ani Watanni 15 A Abuja

Next Post

“Taron Koli Na Demokuradiyya” Da Amurka Ke Gudanarwa Na Cike Da Manufunci Da Girman Kai

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

16 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

18 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

19 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

20 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

2 days ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

2 days ago
Next Post
amurka

“Taron Koli Na Demokuradiyya” Da Amurka Ke Gudanarwa Na Cike Da Manufunci Da Girman Kai

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.