• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin Yin Katsa Landan Ba Zai Dakile Ci Gaban Yankin HK Ba

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
HK
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar dai yadda aka yi tsammani, bayan majalissar dokokin HK ta zartas da kudurin dokar tsaron kasa da gagarumin rinjaye a baya bayan nan, ta kuma cimma nasarar kammala sashe na 23, na dokar gudanarwar yankin na musamman na Sin a ranar 19 ga watan nan, wasu sassa daga kasashen yamma sun zabura, wajen fara sukar wannan mataki, suna masu cewa hanya ce ta dakushe ‘yancin bil adama, kana wasu sun rika nuna shakku, game da yanayin da yankin na HK zai shiga ta fuskar hada hadar kasuwanci.

Amma abun tambaya a nan shi ne, shin wajibi ne a samar da wannan doka ta tsaro? Kuma mene ne ma’anarta ga yankin HK? Alal hakika, zarge-zarge, da kazafi da wadancan sassa suka yiwa Sin ba su da tushe ko makama. Kawai dai akwai wasu mutane a kasashen yamma, dake gudanar da wasan kwaikwayon siyasa da suka saba.

  • Yadda Dimokaradiyya Ke Aiki A Kasar Sin
  • Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2

Ya zuwa yau, mutane sun kara fahimtar wajibcin wannan doka ta tsaron kasa, la’akari da yamutsin da yankin HK ya sha fama da shi mai nasaba da yunkurin “samun ‘yancin kai”, da tashin hankalin da ya biyo bayan hakan, yayin gyaran dokokin jagorancin yankin.

A shekarar 2020 ne aka tsara dokar tsaron kasa ta yankin HK, aka kuma aiwatar da ita, wadda ta zama ginshikin samun wadata da daidaito a yankin. Yanzu haka shekaru 3 sun shude bayan wannan ci gaba, kuma tuni yankin HK ya sauya daga wurin da ya sha fama da tashe tashen hankula, zuwa wuri mai cikakken tsarin jagoranci da walwala. To sai dai kuma a daya hannun, kalubalen tsaron kasa da yankin ke fuskanta har yanzu yana da sarkakiya da tsanani.

Wannan doka ta tsaron kasa ta HK, da sauran dokokin da ake aiwatarwa a yankin na musamman na Sin, ba su kai ga wadatarwa wajen shawo kan dukkanin dabi’u, da ayyuka dake iya haifar da barazana ga tsaron kasa ba. Zartas da wannan doka ta yankin HK a wannan karo, na da nasaba da aiwatar da kudurorin tsaron kasa na HK, da cike gibin manufar tabbatar da tsaro a HK, da tabbatar da wanzuwar daidaito na dogon lokaci a HK, da ma cimma nasarar gudanar da manufar nan ta “kasa daya tsarin mulki biyu” bisa daidaito.  (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Daure Barawon Alkur’ani Watanni 15 A Abuja

Next Post

“Taron Koli Na Demokuradiyya” Da Amurka Ke Gudanarwa Na Cike Da Manufunci Da Girman Kai

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

2 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

4 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

5 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

21 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

21 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

23 hours ago
Next Post
amurka

“Taron Koli Na Demokuradiyya” Da Amurka Ke Gudanarwa Na Cike Da Manufunci Da Girman Kai

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
HK

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.