• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunwa Ba Dimokuradiya Ba Ce

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yunwa Ba Dimokuradiya Ba Ce
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin watsa labarai na BBC, ya watsa wani labari a kwanan nan, wanda ke cewa jama’ar kasashen Larabawa, suna yanke kauna ga tsarin dimokuradiya irin na kasashen yamma. A ganinsu, tsarin ya hana gwamnati taka rawa yadda ake bukata, a fannonin tabbatar da tsaro da raya tattalin arizki.

BBC ya watsa labarin ne, bisa rahoton da kungiyar binciken ra’ayin jama’a ta Arab Barometer ta gabatar, wanda Michael Robbins, shehun malami na jami’ar Princeton ta kasar Amurka, ya wallafa.

  • Sin Ta Dade Tana Taimakawa Afirka Wajen Samun Ci Gaba Mai Dorewa

Shi kuma wannan malami ya rubuta dalilin da ya sa Larabawa suke yanke kauna ga tsarin dimokuradiya na kasashen yamma, wanda shi ne “mutane na fama da yunwa, suna bukatar burodi.”
Cikin shekaru fiye da 10 da suka gabata, an yi jerin juyin juya hali na daukar tsarin dimokuradiya a wasu kasashen Larabawa.

Zuwa yanzu, ko an samu ci gaban harkoki a wadannan kasashe? Amsa ita ce A’a, ba a samu ba!
Idan mun dauki Tunisia, da Lebanon, da Iraki a matsayin misali, a duk wadannan kasashe, an samu sabuwar gwamnati ta hanyar jefa kuri’a, kuma dukkansu sun dauki tsarin dimokuradiya irin na kasashen yamma. Amma zuwa yanzu, jimillar GDP kan kowane mutum a kasar Tunisia ta yi kasa, idan an kwatanta da na shekarar 2011.

Kana kasar Lebanon ma na fuskantar hadarin rushewar tsarin hada-hadar kudi, yayin da kasar Iraki ke fama da matsalar rashin kwanciyar hankali. Duk wadannan abubuwa sun nuna cewa, tsarin dimokuradiya na kasashen yamma, ba wani abu ne dake iya daidaita dukkan matsalolin da ake fuskanta ba.

Labarai Masu Nasaba

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Ban da kasashen Larabawa, ko a kasashen yamma, jama’a suna da cikakken imani game da tsarin dimokuradiya irin nasu? Ko alama! Tsohon dan majalisar dattawan Amurka Tom Daschle, ya rubuta wani bayani a kwanan baya, wanda aka wallafa shi a shafin yanar gizo na majalissun kasar Amurka, inda a ciki yake cewa, tsarin dimokiradiya na kasar Amurka “yana daf da halaka kan sa”, sakamakon wasu manyan matsaloli da suka shafi zaman rayuwar jama’a, irinsu bambancin launin fata, da kisan gillar da ake yi da bindiga, da rashin daidaito a fannin samun kudin shiga, da hauhawar farashin kaya, da annobar COVID-19, da dai sauransu.

Hakika duk wata kasa na da irin nata al’adu, da yanayin kasa, wadanda suka sha bamban da juna. Saboda haka, da wuya a ce akwai wani tsarin siyasa mafi kyau, wanda ya dace da kowa. Da ma dai an gabatar da akidar Dimokuradiya, don tabbatar da cewa gwamnati za ta yi kokarin kare hakkin jama’a ne, da biyan bukatunsu.

Idan ko burodi ma ba ta iya samar musu, ko rayuwa ta zama mai wuya a gare su, ke nan wannan “tsarin dimokuradiya” ba na gaske ba ne. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabon Kamfanin Mai Na NNPC Zai Ceto Makamashin Nijeriya

Next Post

Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)

Related

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

12 hours ago
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

13 hours ago
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

14 hours ago
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan
Daga Birnin Sin

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

14 hours ago
Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan
Daga Birnin Sin

Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

15 hours ago
Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha

16 hours ago
Next Post
Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)

Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kuɓutar Da ‘Yan Ghana 19 Da Aka Yaudare Su Zuwa Nijeriya

July 8, 2025
ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

July 8, 2025
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato

July 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

July 8, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.