• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunwa Ba Dimokuradiya Ba Ce

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yunwa Ba Dimokuradiya Ba Ce
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin watsa labarai na BBC, ya watsa wani labari a kwanan nan, wanda ke cewa jama’ar kasashen Larabawa, suna yanke kauna ga tsarin dimokuradiya irin na kasashen yamma. A ganinsu, tsarin ya hana gwamnati taka rawa yadda ake bukata, a fannonin tabbatar da tsaro da raya tattalin arizki.

BBC ya watsa labarin ne, bisa rahoton da kungiyar binciken ra’ayin jama’a ta Arab Barometer ta gabatar, wanda Michael Robbins, shehun malami na jami’ar Princeton ta kasar Amurka, ya wallafa.

  • Sin Ta Dade Tana Taimakawa Afirka Wajen Samun Ci Gaba Mai Dorewa

Shi kuma wannan malami ya rubuta dalilin da ya sa Larabawa suke yanke kauna ga tsarin dimokuradiya na kasashen yamma, wanda shi ne “mutane na fama da yunwa, suna bukatar burodi.”
Cikin shekaru fiye da 10 da suka gabata, an yi jerin juyin juya hali na daukar tsarin dimokuradiya a wasu kasashen Larabawa.

Zuwa yanzu, ko an samu ci gaban harkoki a wadannan kasashe? Amsa ita ce A’a, ba a samu ba!
Idan mun dauki Tunisia, da Lebanon, da Iraki a matsayin misali, a duk wadannan kasashe, an samu sabuwar gwamnati ta hanyar jefa kuri’a, kuma dukkansu sun dauki tsarin dimokuradiya irin na kasashen yamma. Amma zuwa yanzu, jimillar GDP kan kowane mutum a kasar Tunisia ta yi kasa, idan an kwatanta da na shekarar 2011.

Kana kasar Lebanon ma na fuskantar hadarin rushewar tsarin hada-hadar kudi, yayin da kasar Iraki ke fama da matsalar rashin kwanciyar hankali. Duk wadannan abubuwa sun nuna cewa, tsarin dimokuradiya na kasashen yamma, ba wani abu ne dake iya daidaita dukkan matsalolin da ake fuskanta ba.

Labarai Masu Nasaba

An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 

Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu

Ban da kasashen Larabawa, ko a kasashen yamma, jama’a suna da cikakken imani game da tsarin dimokuradiya irin nasu? Ko alama! Tsohon dan majalisar dattawan Amurka Tom Daschle, ya rubuta wani bayani a kwanan baya, wanda aka wallafa shi a shafin yanar gizo na majalissun kasar Amurka, inda a ciki yake cewa, tsarin dimokiradiya na kasar Amurka “yana daf da halaka kan sa”, sakamakon wasu manyan matsaloli da suka shafi zaman rayuwar jama’a, irinsu bambancin launin fata, da kisan gillar da ake yi da bindiga, da rashin daidaito a fannin samun kudin shiga, da hauhawar farashin kaya, da annobar COVID-19, da dai sauransu.

Hakika duk wata kasa na da irin nata al’adu, da yanayin kasa, wadanda suka sha bamban da juna. Saboda haka, da wuya a ce akwai wani tsarin siyasa mafi kyau, wanda ya dace da kowa. Da ma dai an gabatar da akidar Dimokuradiya, don tabbatar da cewa gwamnati za ta yi kokarin kare hakkin jama’a ne, da biyan bukatunsu.

Idan ko burodi ma ba ta iya samar musu, ko rayuwa ta zama mai wuya a gare su, ke nan wannan “tsarin dimokuradiya” ba na gaske ba ne. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabon Kamfanin Mai Na NNPC Zai Ceto Makamashin Nijeriya

Next Post

Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)

Related

An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 
Daga Birnin Sin

An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 

7 minutes ago
Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu

1 hour ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu

19 hours ago
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

20 hours ago
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU
Daga Birnin Sin

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

21 hours ago
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

22 hours ago
Next Post
Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)

Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)

LABARAI MASU NASABA

An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 

An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 

August 14, 2025
‘Yan Majalisa Na Ba Da Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Iya Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.

‘Yan Majalisa Na Ba Da Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Iya Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.

August 14, 2025
Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu

Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu

August 14, 2025
An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara

August 14, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutum 2 Da Bindigogi Da Alburusai A Filato

’Yansanda Sun Kama Mutum 2 Da Bindigogi Da Alburusai A Filato

August 14, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

August 14, 2025
An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

August 14, 2025
Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

August 14, 2025
Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

August 14, 2025
Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.